Noor
Hausa
Noor / Addu'a / Yabon Allah / Istigfari da tuba

Istigfari da tuba

Yabon Allah · addu'o'i 6

Istigfari da tuba 0:00
Saurara
1

قَالَ رَسُولُ اللَّهِ صلى الله عليه وسلم: وَاللَّهِ إِنِّي لأَسْتَغفِرُ اللَّهَ وَأَتُوبُ إِلَيْهِ فِي الْيَوْمِ أَكْثَرَ مِنْ سَبْعِينَ مَرَّةٍ

Ma’ana: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Ina rantsuwa da Allah, lalle ni ina neman gafarar Allah kuma ina tuba gare shi a kowacce rana sama da sau saba’in.

Majiya: Al-Bukhari.

2

وَقَالَ صلى الله عليه وسلم: يَا أَيُّهَا النَّاسُ تُوبُوا إِلَى اللَّهِ فَإِنِّي أَتُوبُ فِي الْيَوْمِ إِلَيْهِ مِائَةَ مَرَّةٍ

Ma’ana: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Ku tuba zuwa ga Allah domin ni ina tuba a kowace rana zuwa gare shi sau dari.

Majiya: Muslim 4/2076.

3

وَقَالَ صلى الله عليه وسلم: مَنْ قَالَ أَسْتَغْفِرُ اللَّهَ الْعَظيمَ الَّذِي لاَ إِلَهَ إِلاَّ هُوَ الْحَيُّ القَيّوُمُ وَأَتُوبُ إِلَيهِ, غَفَرَ اللَّهُ لَهُ وَإِنْ كَانَ فَرَّ مِنَ الزَّحْفِ

Ma’ana: Ina neman gafarar Allah, wanda babu abin bautawa da cancanta sai shi, Rayayye, Tsayayye (wanda kowa ya tsayu da shi), kuma ina tuba zuwa gare shi. Allah zai gafarta masa zunuban sa ko da ya gudu daga fagen fama ne.

Majiya: Abu Dawud 2/85, At-Tirmizi 5/569, Al-Hakim.

4

وَقَالَ صلى الله عليه وسلم: أَقْرَبُ مَا يَكُونُ الرَّبُّ مِنَ الْعَبْدِ فِي جَوْفِ اللَّيْلِ الآخِرِ فَإِنِ اسْتَطَعْتَ أَنْ تَكُونَ مِمَّنْ يَذْكُرُ اللَّهَ فِي تِلْكَ السَّاعَةِ فَكُنْ

Ma’ana: Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Mafi kusanci da Allah yake kasancewa da bawansa shi ne a tsakiyar karshen darene. Don haka Idan kana da ikon kasancewa cikin masu ambaton Allah a wannan lokacin to ka kasance.

Majiya: At-Tirmizi, An-Nasa'i 1/279 and Al-Hakim.

5

وَقَالَ صلى الله عليه وسلم: أَقْرَبُ مَا يَكُونُ الْعَبْدُ مِنْ رَبِّهِ وَهُوَ سَاجِدٌ فَأَكثِرُوا الدُّعَاءَ

Ma’ana: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Mafi kusancin da bawa zai kasance da Allah Ubangijinsa shi ne lokacin da bawansa yake sujada, don haka ku ya waita addu’a. (A cikin sujada)

Majiya: Muslim 1/350.

6

وَقَالَ صلى الله عليه وسلم: إِنَّهُ لَيُغَانُ عَلَى قَلْبِي وَإِنِّي لأَسْتَغْفِرُ اللَّهَ فِي الْيَوْمِ مِائَةَ مَرَّةٍ

Ma’ana: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce. “Hakika a kan lullube zuciyata, kuma ni ina neman gafarar Allaha sau dari a rana.

Majiya: Muslim 4/2075.