Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Shu'ara
26

Shu'ara — Mawaƙa

الشُّعَرَاءِ
Makkiyya Aya 227
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

طسٓمٓ

Taa-Seeen-Meeem

¦. S̃. M̃.

Aya 2

تِلْكَ ءَايَٰتُ ٱلْكِتَٰبِ ٱلْمُبِينِ

Tilka Aayaatul Kitaabil Mubeen

Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.

Aya 3

لَعَلَّكَ بَٰخِعٌۭ نَّفْسَكَ أَلَّا يَكُونُوا۟ مُؤْمِنِينَ

La'allaka baakhi'un nafsaka allaa yakoonoo mu'mineen

Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!

Aya 4

إِن نَّشَأْ نُنَزِّلْ عَلَيْهِم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ ءَايَةًۭ فَظَلَّتْ أَعْنَٰقُهُمْ لَهَا خَٰضِعِينَ

In nashaa nunazzil 'alaihim minas samaaa'i Aayatan fazallat a'naaquhum lahaa khaadi'een

Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.

Aya 5

وَمَا يَأْتِيهِم مِّن ذِكْرٍۢ مِّنَ ٱلرَّحْمَٰنِ مُحْدَثٍ إِلَّا كَانُوا۟ عَنْهُ مُعْرِضِينَ

Wa maa yaateehim min zikrim minar Rahmaani muhdasin illaa kaanoo 'anhu mu'rideen

Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.

Aya 6

فَقَدْ كَذَّبُوا۟ فَسَيَأْتِيهِمْ أَنۢبَٰٓؤُا۟ مَا كَانُوا۟ بِهِۦ يَسْتَهْزِءُونَ

Faqad kazzaboo fasa yaateehim ambaaa'u maa kaanoo bihee yastahzi'oon

To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.

Aya 7

أَوَلَمْ يَرَوْا۟ إِلَى ٱلْأَرْضِ كَمْ أَنۢبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوْجٍۢ كَرِيمٍ

Awa lam yaraw ilal ardi kam ambatnaa feehaa min kulli zawjin kareem

Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?

Aya 8

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَءَايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

Inn fee zaalika la Aayah; wa maa kaana aksaruhum mu'mineen

Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.

Aya 9

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Wa inna Rabbaka la Huwal 'Azeezur Raheem

Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.

Aya 10

وَإِذْ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱئْتِ ٱلْقَوْمَ ٱلظَّٰلِمِينَ

Wa iz naadaa Rabbuka Moosaaa ani'-til qawmaz zaalimeen

Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.

Aya 11

قَوْمَ فِرْعَوْنَ ۚ أَلَا يَتَّقُونَ

Qawma Fir'awn; alaa yattaqoon

"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"

Aya 12

قَالَ رَبِّ إِنِّىٓ أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ

Qaala Rabbi inneee akhaafu ai yukazziboon

Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.

Aya 13

وَيَضِيقُ صَدْرِى وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِى فَأَرْسِلْ إِلَىٰ هَٰرُونَ

Wa yadeequ sadree wa laa yantaliqu lisaanee fa arsil ilaa Haaroon

"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.

Aya 14

وَلَهُمْ عَلَىَّ ذَنۢبٌۭ فَأَخَافُ أَن يَقْتُلُونِ

Wa lahum 'alaiya zambun fa akhaafu ai yaqtuloon

"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."

Aya 15

قَالَ كَلَّا ۖ فَٱذْهَبَا بِـَٔايَٰتِنَآ ۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسْتَمِعُونَ

Qaala kallaa fazhabaa bi Aayaatinaaa innaa ma'akum mustami'oon

Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."

Aya 16

فَأْتِيَا فِرْعَوْنَ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولُ رَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Faatiyaa Fir'awna faqoolaaa innaa Rasoolu Rabbil 'aalameen

"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."

Aya 17

أَنْ أَرْسِلْ مَعَنَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ

An arsil ma'anaa Baneee Israaa'eel

"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."

Aya 18

قَالَ أَلَمْ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدًۭا وَلَبِثْتَ فِينَا مِنْ عُمُرِكَ سِنِينَ

Qaala alam nurabbika feenaa waleedanw wa labista feenaa min 'umurika sineen

Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"

Aya 19

وَفَعَلْتَ فَعْلَتَكَ ٱلَّتِى فَعَلْتَ وَأَنتَ مِنَ ٱلْكَٰفِرِينَ

Wa fa'alta fa'latakal latee fa'alta wa anta minal kaafireen

"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"

Aya 20

قَالَ فَعَلْتُهَآ إِذًۭا وَأَنَا۠ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ

Qaala fa'altuhaaa izanw wa ana minad daaaleen

Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."

Aya 21

فَفَرَرْتُ مِنكُمْ لَمَّا خِفْتُكُمْ فَوَهَبَ لِى رَبِّى حُكْمًۭا وَجَعَلَنِى مِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

Fafarartu minkum lam maa khiftukum fawahaba lee Rabbee hukmanw wa ja'alanee minal mursaleen

"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."

Aya 22

وَتِلْكَ نِعْمَةٌۭ تَمُنُّهَا عَلَىَّ أَنْ عَبَّدتَّ بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ

Wa tilka ni'matun tamun nuhaa 'alaiya an 'abbatta Baneee Israaa'eel

"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."

Aya 23

قَالَ فِرْعَوْنُ وَمَا رَبُّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Qaala Fir'awnu wa maa Rabbul 'aalameen

Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"

Aya 24

قَالَ رَبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَآ ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ

Qaala Rabbus samaawaati wal ardi wa maa bainahumaa in kuntum mooqineen

Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."

Aya 25

قَالَ لِمَنْ حَوْلَهُۥٓ أَلَا تَسْتَمِعُونَ

Qaala liman hawlahooo alaa tastami'oon

Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"

Aya 26

قَالَ رَبُّكُمْ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ

Qaala Rabbukum wa Rabbu aabaaa'ikumul awwaleen

Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."

Aya 27

قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ ٱلَّذِىٓ أُرْسِلَ إِلَيْكُمْ لَمَجْنُونٌۭ

Qaala inna Rasoolakumul lazee ursila ilaikum lamajnoon

Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."

Aya 28

قَالَ رَبُّ ٱلْمَشْرِقِ وَٱلْمَغْرِبِ وَمَا بَيْنَهُمَآ ۖ إِن كُنتُمْ تَعْقِلُونَ

Qaala Rabbul mashriqi wal maghribi wa maa baina humaa in kuntum ta'qiloon

Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."

Aya 29

قَالَ لَئِنِ ٱتَّخَذْتَ إِلَٰهًا غَيْرِى لَأَجْعَلَنَّكَ مِنَ ٱلْمَسْجُونِينَ

Qaala la'init takhazta ilaahan ghairee la aj'alannaka minal masjooneen

Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."

Aya 30

قَالَ أَوَلَوْ جِئْتُكَ بِشَىْءٍۢ مُّبِينٍۢ

Qaala awalw ji'tuka bishai'im mubeen

Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"

Aya 31

قَالَ فَأْتِ بِهِۦٓ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّٰدِقِينَ

Qaala faati biheee in kunta minas saadiqeen

Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."

Aya 32

فَأَلْقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِىَ ثُعْبَانٌۭ مُّبِينٌۭ

Fa alqaa 'asaahu fa izaaa hiya su'baanum mubeen

Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.

Aya 33

وَنَزَعَ يَدَهُۥ فَإِذَا هِىَ بَيْضَآءُ لِلنَّٰظِرِينَ

Wa naza'a yadahoo faizaa hiya baidaaa'u linnaa zireen

Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.

Aya 34

قَالَ لِلْمَلَإِ حَوْلَهُۥٓ إِنَّ هَٰذَا لَسَٰحِرٌ عَلِيمٌۭ

Qaala lilmala-i hawlahooo inna haazaa lasaahirun 'aleem

(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!

Aya 35

يُرِيدُ أَن يُخْرِجَكُم مِّنْ أَرْضِكُم بِسِحْرِهِۦ فَمَاذَا تَأْمُرُونَ

Yureedu ai yukhrijakum min ardikum bisihrihee famaazaa taamuroon

"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"

Aya 36

قَالُوٓا۟ أَرْجِهْ وَأَخَاهُ وَٱبْعَثْ فِى ٱلْمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ

Qaalooo arjih wa akhaahu wab'as filmadaaa'ini haashireen

Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."

Aya 37

يَأْتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٍۢ

Yaatooka bikulli sah haarin 'aleem

"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."

Aya 38

فَجُمِعَ ٱلسَّحَرَةُ لِمِيقَٰتِ يَوْمٍۢ مَّعْلُومٍۢ

Fa jumi'as saharatu limeeqaati Yawmim ma'loom

Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.

Aya 39

وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلْ أَنتُم مُّجْتَمِعُونَ

Wa qeela linnaasi hal antum mujtami'oon

Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?

Aya 40

لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ ٱلسَّحَرَةَ إِن كَانُوا۟ هُمُ ٱلْغَٰلِبِينَ

La'allanaa nattabi'us saharata in kaanoo humul ghaalibeen

"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."

Aya 41

فَلَمَّا جَآءَ ٱلسَّحَرَةُ قَالُوا۟ لِفِرْعَوْنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجْرًا إِن كُنَّا نَحْنُ ٱلْغَٰلِبِينَ

Falammaa jaaa'as saharatu qaaloo li Fir'awna a'inna lanaa la ajjran in kunnaa nahnul ghaalibeen

To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"

Aya 42

قَالَ نَعَمْ وَإِنَّكُمْ إِذًۭا لَّمِنَ ٱلْمُقَرَّبِينَ

Qaala na'am wa innakum izal laminal muqarrabeen

Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."

Aya 43

قَالَ لَهُم مُّوسَىٰٓ أَلْقُوا۟ مَآ أَنتُم مُّلْقُونَ

Qaala lahum Moosaaa alqoo maaa antum mulqoon

Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."

Aya 44

فَأَلْقَوْا۟ حِبَالَهُمْ وَعِصِيَّهُمْ وَقَالُوا۟ بِعِزَّةِ فِرْعَوْنَ إِنَّا لَنَحْنُ ٱلْغَٰلِبُونَ

Fa alqaw hibaalahum wa 'isiyyahum wa qaaloo bi'izzati Fir'awna innaa lanahnul ghaaliboon

Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."

Aya 45

فَأَلْقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِىَ تَلْقَفُ مَا يَأْفِكُونَ

Fa alqaa Moosaa 'asaahu fa izaa hiya talqafu maa yaafikoon

Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.

Aya 46

فَأُلْقِىَ ٱلسَّحَرَةُ سَٰجِدِينَ

Fa ulqiyas saharatu saajideen

Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.

Aya 47

قَالُوٓا۟ ءَامَنَّا بِرَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Qaalooo aamannaa bi Rabbil 'aalameen

Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."

Aya 48

رَبِّ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

Rabbi Moosaa wa Haaroon

"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."

Aya 49

قَالَ ءَامَنتُمْ لَهُۥ قَبْلَ أَنْ ءَاذَنَ لَكُمْ ۖ إِنَّهُۥ لَكَبِيرُكُمُ ٱلَّذِى عَلَّمَكُمُ ٱلسِّحْرَ فَلَسَوْفَ تَعْلَمُونَ ۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيْدِيَكُمْ وَأَرْجُلَكُم مِّنْ خِلَٰفٍۢ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمْ أَجْمَعِينَ

Qaala aamantum lahoo qabla an aazana lakum innahoo lakabeerukumul lazee 'alla makumus sihra falasawfa ta'lamoon; la uqatti'anna aidiyakum wa arjulakum min khilaafinw wa la usallibanna kum ajma'een

Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."

Aya 50

قَالُوا۟ لَا ضَيْرَ ۖ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ

Qaaloo la daira innaaa ilaa Rabbinaa munqalliboon

Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."

Aya 51

إِنَّا نَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَٰيَٰنَآ أَن كُنَّآ أَوَّلَ ٱلْمُؤْمِنِينَ

Innaa natma'u ai yaghfira lanaa Rabbunna khataa yaanaaa an kunnaaa awwalal mu'mineen

"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."

Aya 52

۞ وَأَوْحَيْنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنْ أَسْرِ بِعِبَادِىٓ إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ

Wa awhainaaa ilaa Moosaaa an asri bi'ibaadeee innakum muttaba'oon

Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã ne.

Aya 53

فَأَرْسَلَ فِرْعَوْنُ فِى ٱلْمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ

Fa arsala Fir'awnu filmadaaa'ini haashireen

Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.

Aya 54

إِنَّ هَٰٓؤُلَآءِ لَشِرْذِمَةٌۭ قَلِيلُونَ

Inna haaa'ulaaa'i lashir zimatun qaleeloon

"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."

Aya 55

وَإِنَّهُمْ لَنَا لَغَآئِظُونَ

Wa innahum lanaa laghaaa'izoon

"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."

Aya 56

وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَٰذِرُونَ

Wa innaa lajamee'un haaziroon

"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."

Aya 57

فَأَخْرَجْنَٰهُم مِّن جَنَّٰتٍۢ وَعُيُونٍۢ

Fa akhrajnaahum min Jannaatinw wa 'uyoon

Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.

Aya 58

وَكُنُوزٍۢ وَمَقَامٍۢ كَرِيمٍۢ

Wa kunoozinw wa ma qaamin kareem

Da taskõki da mazauni mai kyau.

Aya 59

كَذَٰلِكَ وَأَوْرَثْنَٰهَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ

Kazaalika wa awrasnaahaa Baneee Israaa'eel

Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.

Aya 60

فَأَتْبَعُوهُم مُّشْرِقِينَ

Fa atba'oohum mushriqeen

Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.

Aya 61

فَلَمَّا تَرَٰٓءَا ٱلْجَمْعَانِ قَالَ أَصْحَٰبُ مُوسَىٰٓ إِنَّا لَمُدْرَكُونَ

Falammaa taraaa'al jam'aani qaala as haabu Moosaaa innaa lamudrakoon

Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."

Aya 62

قَالَ كَلَّآ ۖ إِنَّ مَعِىَ رَبِّى سَيَهْدِينِ

Qaala kallaaa inna ma'iya Rabbee sa yahdeen

Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."

Aya 63

فَأَوْحَيْنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضْرِب بِّعَصَاكَ ٱلْبَحْرَ ۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرْقٍۢ كَٱلطَّوْدِ ٱلْعَظِيمِ

Fa awhainaaa ilaa Moosaaa anidrib bi'asaakal bahra fanfalaqa fakaana kullu firqin kattawdil 'azeem

Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge, kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.

Aya 64

وَأَزْلَفْنَا ثَمَّ ٱلْءَاخَرِينَ

Wa azlafnaa sammal aakhareen

Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.

Aya 65

وَأَنجَيْنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجْمَعِينَ

Wa anjainaa Moosaa wa mam ma'ahooo ajma'een

Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.

Aya 66

ثُمَّ أَغْرَقْنَا ٱلْءَاخَرِينَ

Summa aghraqnal aakhareen

Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.

Aya 67

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَءَايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

Inna fee zaalika la Aayaah; wa maa kaana aksaru hu mu'mineen

Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Aya 68

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Wa inna Rabbaka la Huwal 'Azeezur Raheem

Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.

Aya 69

وَٱتْلُ عَلَيْهِمْ نَبَأَ إِبْرَٰهِيمَ

Watlu 'alaihim naba-a Ibraaheem

Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.

Aya 70

إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِۦ مَا تَعْبُدُونَ

Iz qaala li abeehi wa qawmihee maa ta'budoon

A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"

Aya 71

قَالُوا۟ نَعْبُدُ أَصْنَامًۭا فَنَظَلُّ لَهَا عَٰكِفِينَ

Qaaloo na'budu asnaaman fanazallu lahaa 'aakifeen

Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."

Aya 72

قَالَ هَلْ يَسْمَعُونَكُمْ إِذْ تَدْعُونَ

Qaala hal yasma'oona kum iz tad'oon

Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"

Aya 73

أَوْ يَنفَعُونَكُمْ أَوْ يَضُرُّونَ

Aw yanfa'oonakum aw yadurroon

"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"

Aya 74

قَالُوا۟ بَلْ وَجَدْنَآ ءَابَآءَنَا كَذَٰلِكَ يَفْعَلُونَ

Qaaloo bal wajadnaaa aabaaa 'anaa kazaalika yaf'aloon

Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."

Aya 75

قَالَ أَفَرَءَيْتُم مَّا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ

Qaala afara 'aitum maa kuntum ta'budoon

Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"

Aya 76

أَنتُمْ وَءَابَآؤُكُمُ ٱلْأَقْدَمُونَ

Antum wa aabaaa'ukumul aqdamoon

"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"

Aya 77

فَإِنَّهُمْ عَدُوٌّۭ لِّىٓ إِلَّا رَبَّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Fa innahum 'aduwwwul leee illaa Rabbal 'aalameen

"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."

Aya 78

ٱلَّذِى خَلَقَنِى فَهُوَ يَهْدِينِ

Allazee khalaqanee fa Huwa yahdeen

"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."

Aya 79

وَٱلَّذِى هُوَ يُطْعِمُنِى وَيَسْقِينِ

Wallazee Huwa yut'imunee wa yasqeen

"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."

Aya 80

وَإِذَا مَرِضْتُ فَهُوَ يَشْفِينِ

Wa izaa mardtu fahuwa yashfeen

"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."

Aya 81

وَٱلَّذِى يُمِيتُنِى ثُمَّ يُحْيِينِ

Wallazee yumeetunee summa yuhyeen

"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."

Aya 82

وَٱلَّذِىٓ أَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لِى خَطِيٓـَٔتِى يَوْمَ ٱلدِّينِ

Wallazeee atma'u ai yaghfira lee khateee' atee Yawmad Deen

"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."

Aya 83

رَبِّ هَبْ لِى حُكْمًۭا وَأَلْحِقْنِى بِٱلصَّٰلِحِينَ

Rabbi hab lee hukmanw wa alhiqnee bis saaliheen

"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."

Aya 84

وَٱجْعَل لِّى لِسَانَ صِدْقٍۢ فِى ٱلْءَاخِرِينَ

Waj'al lee lisaana sidqin fil aakhireen

"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutãnen ƙarshe."

Aya 85

وَٱجْعَلْنِى مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ ٱلنَّعِيمِ

Waj'alnee minw warasati Jannnatin Na'eem

"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."

Aya 86

وَٱغْفِرْ لِأَبِىٓ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ

Waghfir li abeee innahoo kaana mind daalleen

"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."

Aya 87

وَلَا تُخْزِنِى يَوْمَ يُبْعَثُونَ

Wa laa tukhzinee Yawma yub'asoon

"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."

Aya 88

يَوْمَ لَا يَنفَعُ مَالٌۭ وَلَا بَنُونَ

Yawma laa yanfa'u maalunw wa laa banoon

"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."

Aya 89

إِلَّا مَنْ أَتَى ٱللَّهَ بِقَلْبٍۢ سَلِيمٍۢ

Illaa man atal laaha biqalbin saleem

"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."

Aya 90

وَأُزْلِفَتِ ٱلْجَنَّةُ لِلْمُتَّقِينَ

Wa uzlifatil Jannatu lilmuttaqeen

Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.

Aya 91

وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِلْغَاوِينَ

Wa burrizatil Jaheemu lilghaaween

Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.

Aya 92

وَقِيلَ لَهُمْ أَيْنَ مَا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ

Wa qeela lahum aina maa kuntum ta'budoon

Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"

Aya 93

مِن دُونِ ٱللَّهِ هَلْ يَنصُرُونَكُمْ أَوْ يَنتَصِرُونَ

Min doonil laahi hal yansuroonakum aw yantasiroon

"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"

Aya 94

فَكُبْكِبُوا۟ فِيهَا هُمْ وَٱلْغَاوُۥنَ

Fakubkiboo feehaa hum walghaawoon

Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun.

Aya 95

وَجُنُودُ إِبْلِيسَ أَجْمَعُونَ

Wa junoodu Ibleesa ajma'oon

Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.

Aya 96

قَالُوا۟ وَهُمْ فِيهَا يَخْتَصِمُونَ

Qaaloo wa hum feehaa yakkhtasimoon

Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,

Aya 97

تَٱللَّهِ إِن كُنَّا لَفِى ضَلَٰلٍۢ مُّبِينٍ

Tallaahi in kunnaa lafee dalaalim mubeen

"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."

Aya 98

إِذْ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Iz nusawweekum bi Rabbil 'aalameen

"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.

Aya 99

وَمَآ أَضَلَّنَآ إِلَّا ٱلْمُجْرِمُونَ

Wa maaa adallanaaa illal mujrimoon

"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."

Aya 100

فَمَا لَنَا مِن شَٰفِعِينَ

Famaa lanaa min shaa fi'een

"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."

Aya 101

وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٍۢ

Wa laa sadeeqin hameem

"Kuma bã mu da abõki, masõyi."

Aya 102

فَلَوْ أَنَّ لَنَا كَرَّةًۭ فَنَكُونَ مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ

Falaw anna lanaa karratan fanakoona minal mu'mineen

"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"

Aya 103

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَءَايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

Inna fee zaalika la Aayatanw wa maa kaana aksaruhum mu'mineen

Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.

Aya 104

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Wa inna Rabbaka la Huwal 'Azeezur Raheem

Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Aya 105

كَذَّبَتْ قَوْمُ نُوحٍ ٱلْمُرْسَلِينَ

Kazzabat qawmu Noohinil Mursaleen

Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.

Aya 106

إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Iz qaala lahum akhoohum Noohun alaa tattaqoon

A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"

Aya 107

إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ

Innee lakum Rasoolun ameen

"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."

Aya 108

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

Fattaqullaaha wa atee'oon

"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Aya 109

وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Wa maaa as'alukum 'alaihi min ajrin in ajriya illaa 'alaa Rabbil 'aalameen

"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

Aya 110

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

Fattaqul laaha wa atee'oon

"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Aya 111

۞ قَالُوٓا۟ أَنُؤْمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلْأَرْذَلُونَ

Qaalooo anu'minu laka wattaba 'akal arzaloon

Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"

Aya 112

قَالَ وَمَا عِلْمِى بِمَا كَانُوا۟ يَعْمَلُونَ

Qaala wa maa 'ilmee bimaa kaanoo ya'maloon

Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."

Aya 113

إِنْ حِسَابُهُمْ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّى ۖ لَوْ تَشْعُرُونَ

In hisaabuhum illaa 'alaa Rabbee law tash'uroon

"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."

Aya 114

وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلْمُؤْمِنِينَ

Wa maaa ana bitaaridil mu'mineen

"Ban zama mai kõre mũminai ba."

Aya 115

إِنْ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٌۭ مُّبِينٌۭ

In ana illaa nazeerum mubeen

"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."

Aya 116

قَالُوا۟ لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَٰنُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلْمَرْجُومِينَ

Qaaloo la'il lam tantahi yaa Noohu latakoonanna minal marjoomeen

Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"

Aya 117

قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوْمِى كَذَّبُونِ

Qaala Rabbi inna qawmee kazzaboon

Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."

Aya 118

فَٱفْتَحْ بَيْنِى وَبَيْنَهُمْ فَتْحًۭا وَنَجِّنِى وَمَن مَّعِىَ مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ

Faftab bainee wa bai nahum fat hanw wa najjinee wa mam ma'iya minal mu'mineen

"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."

Aya 119

فَأَنجَيْنَٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِى ٱلْفُلْكِ ٱلْمَشْحُونِ

Fa anjainaahu wa mamma'ahoo fil fulkil mashhoon

Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.

Aya 120

ثُمَّ أَغْرَقْنَا بَعْدُ ٱلْبَاقِينَ

Summa aghraqnaa ba'dul baaqeen

Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.

Aya 121

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَءَايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

Inna fee zaalika la Aayaah; wa maa kaana aksaruhum mu'mineen

Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Aya 122

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Wa inna Rabbaka la huwal 'Azeezur Raheem

Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.

Aya 123

كَذَّبَتْ عَادٌ ٱلْمُرْسَلِينَ

Kazzabat 'Aadunil mursaleen

Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.

Aya 124

إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Iz qaala lahum akhoohum Hoodun alaa tattaqoon

A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

Aya 125

إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ

Innee lakum Rasoolun ameen

"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."

Aya 126

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

Fattaqullaaha wa atee'oon

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Aya 127

وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Wa maa as'alukum 'alaihi min ajrin in ajriya illaa 'alaa Rabbil 'aalameen

"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."

Aya 128

أَتَبْنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ ءَايَةًۭ تَعْبَثُونَ

Atabnoona bikulli ree'in aayatan ta'basoon

"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"

Aya 129

وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمْ تَخْلُدُونَ

Wa tattakhizoona masaani'a la'allakum takhludoon

"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"

Aya 130

وَإِذَا بَطَشْتُم بَطَشْتُمْ جَبَّارِينَ

Wa izaa batashtum batashtum jabbaareen

"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."

Aya 131

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

Fattaqul laaha wa atee'oon

"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Aya 132

وَٱتَّقُوا۟ ٱلَّذِىٓ أَمَدَّكُم بِمَا تَعْلَمُونَ

Wattaqul lazeee amad dakum bimaa ta'lamoon

"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."

Aya 133

أَمَدَّكُم بِأَنْعَٰمٍۢ وَبَنِينَ

Amaddakum bi an'aa minw wa baneen

"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."

Aya 134

وَجَنَّٰتٍۢ وَعُيُونٍ

Wa jannaatinw wa 'uyoon

"Da gõnaki da marẽmari."

Aya 135

إِنِّىٓ أَخَافُ عَلَيْكُمْ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍۢ

Innee akhaafu 'alaikum 'azaaba Yawmin 'azeem

"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."

Aya 136

قَالُوا۟ سَوَآءٌ عَلَيْنَآ أَوَعَظْتَ أَمْ لَمْ تَكُن مِّنَ ٱلْوَٰعِظِينَ

Qaaloo sawaaa'un 'alainaaa awa 'azta am lam takum minal waa'izeen

Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."

Aya 137

إِنْ هَٰذَآ إِلَّا خُلُقُ ٱلْأَوَّلِينَ

In haazaaa illaa khuluqul awwaleen

"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen mutãnen farko."

Aya 138

وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ

Wa maa nahnu bimu 'azzabeen

"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."

Aya 139

فَكَذَّبُوهُ فَأَهْلَكْنَٰهُمْ ۗ إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَءَايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

Fakazzaboohu fa ahlaknaahum; inna fee zaalika la aayah; wa maa kaana aksaruhum mu'mineen

Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Aya 140

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Wa inna Rabbaka la huwal 'Azeezur Raheem

Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Aya 141

كَذَّبَتْ ثَمُودُ ٱلْمُرْسَلِينَ

Kazzabat Samoodul mursaleen

Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.

Aya 142

إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ صَٰلِحٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Iz qaala lahum akhoohum Saalihun alaa tattaqoon

A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"

Aya 143

إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ

Innee lakum Rasoolun ameen

"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."

Aya 144

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

Fattaqul laaha wa atee'oon

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.

Aya 145

وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Wa maaa as'alukum 'alaihi min ajrin in ajriya illaa 'alaa Rabbil 'aalameen

"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."

Aya 146

أَتُتْرَكُونَ فِى مَا هَٰهُنَآ ءَامِنِينَ

Atutrakoona fee maa haahunnaaa aamineen

"Shin, anã barin ku a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"

Aya 147

فِى جَنَّٰتٍۢ وَعُيُونٍۢ

Fee jannaatinw wa 'uyoon

"A cikin gõnaki da marẽmari."

Aya 148

وَزُرُوعٍۢ وَنَخْلٍۢ طَلْعُهَا هَضِيمٌۭ

Wa zuroo inw wa nakhlin tal 'uhaa hadeem

"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?"

Aya 149

وَتَنْحِتُونَ مِنَ ٱلْجِبَالِ بُيُوتًۭا فَٰرِهِينَ

Wa tanhitoona minal jibaali buyootan faariheen

"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"

Aya 150

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

Fattaqul laaha wa atee'oon

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Aya 151

وَلَا تُطِيعُوٓا۟ أَمْرَ ٱلْمُسْرِفِينَ

Wa laa tutee'ooo amral musrifeen

"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."

Aya 152

ٱلَّذِينَ يُفْسِدُونَ فِى ٱلْأَرْضِ وَلَا يُصْلِحُونَ

Allazeena yufsidoona fil ardi wa laa yuslihoon

"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."

Aya 153

قَالُوٓا۟ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلْمُسَحَّرِينَ

Qaalooo innamaa anta minal musahhareen

Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."

Aya 154

مَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٌۭ مِّثْلُنَا فَأْتِ بِـَٔايَةٍ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّٰدِقِينَ

Maaa anta illaa basharum mislunaa faati bi Aayatin in kunta minas saadiqeen

"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."

Aya 155

قَالَ هَٰذِهِۦ نَاقَةٌۭ لَّهَا شِرْبٌۭ وَلَكُمْ شِرْبُ يَوْمٍۢ مَّعْلُومٍۢ

Qaala haazihee naaqatul lahaa shirbunw w alakum shirbu yawmim ma'loom

Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan yini, kuma kunã da shan yini sasanne."

Aya 156

وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٍۢ فَيَأْخُذَكُمْ عَذَابُ يَوْمٍ عَظِيمٍۢ

Wa laa tamassoohaa bisooo'in fa yaakhuzakum 'azaabu Yawmin 'Azeem

"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."

Aya 157

فَعَقَرُوهَا فَأَصْبَحُوا۟ نَٰدِمِينَ

Fa'aqaroohaa fa asbahoo naadimeen

Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.

Aya 158

فَأَخَذَهُمُ ٱلْعَذَابُ ۗ إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَءَايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

Fa akhazahumul 'azaab; inna fee zaalika la Aayah; wa maa kaana aksaruhum m'mineen

Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Aya 159

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Wa inna Rabbaka la Huwal 'Azeezur Raheem

Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.

Aya 160

كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍ ٱلْمُرْسَلِينَ

kazzabat qawmu Lootinil mursaleen

Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.

Aya 161

إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Iz qaala lahum akhoohum Lootun alaa tattaqoon

A lõkacin da ɗan'uwansu, Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

Aya 162

إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ

Innee lakum rasoolun ameen

"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."

Aya 163

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

Fattaqul laaha wa atee'oon

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Aya 164

وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Wa maaa as'alukum 'alaihi min ajrin in ajriya illaa 'alaa Rabbil 'aalameen

"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

Aya 165

أَتَأْتُونَ ٱلذُّكْرَانَ مِنَ ٱلْعَٰلَمِينَ

Ataatoonaz zukraana minal 'aalameen

"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"

Aya 166

وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمْ رَبُّكُم مِّنْ أَزْوَٰجِكُم ۚ بَلْ أَنتُمْ قَوْمٌ عَادُونَ

Wa tazaroona maa khalaqa lakum Rabbukum min azwaajikum; bal antum qawmun 'aadoon

"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"

Aya 167

قَالُوا۟ لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَٰلُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلْمُخْرَجِينَ

Qaloo la'il lam tantahi yaa Lootu latakoonanna minal mukhrajeen

Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."

Aya 168

قَالَ إِنِّى لِعَمَلِكُم مِّنَ ٱلْقَالِينَ

Qaala innee li'amalikum minal qaaleen

Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."

Aya 169

رَبِّ نَجِّنِى وَأَهْلِى مِمَّا يَعْمَلُونَ

Rabbi najjjinee wa ahlee mimmmaa ya'maloon

"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."

Aya 170

فَنَجَّيْنَٰهُ وَأَهْلَهُۥٓ أَجْمَعِينَ

Fanajjainaahu wa ahlahooo ajma'een

Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.

Aya 171

إِلَّا عَجُوزًۭا فِى ٱلْغَٰبِرِينَ

Illaa 'ajoozan filghaabireen

Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.

Aya 172

ثُمَّ دَمَّرْنَا ٱلْءَاخَرِينَ

Summa dammarnal aa khareen

Sa'an nan kuma Muka darkãke wasu.

Aya 173

وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِم مَّطَرًۭا ۖ فَسَآءَ مَطَرُ ٱلْمُنذَرِينَ

Wa amtarnaa 'alaihim mataran fasaaa'a matarul munzareen

Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.

Aya 174

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَءَايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

Inna fee zaalika la Aayah; wa maa kaana aksaruhum mu'mineen

Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.

Aya 175

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Wa inna Rabbaka la Huwal 'Azeezur Raheem

Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Aya 176

كَذَّبَ أَصْحَٰبُ لْـَٔيْكَةِ ٱلْمُرْسَلِينَ

Kazzaba As haabul Aykatil mursaleen

Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.

Aya 177

إِذْ قَالَ لَهُمْ شُعَيْبٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Iz qaala lahum Shu'aybun alaa tattaqoon

A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

Aya 178

إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ

Innee lakum Rasoolun ameen

"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."

Aya 179

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

Fattaqul laaha wa atee'oon

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."

Aya 180

وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Wa maaa as'alukum 'alaihi min ajrin in ajriya illaa 'alaa Rabbil 'aalameen

"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

Aya 181

۞ أَوْفُوا۟ ٱلْكَيْلَ وَلَا تَكُونُوا۟ مِنَ ٱلْمُخْسِرِينَ

Awful kaila wa laa takoonoo minal mukhsireen

"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."

Aya 182

وَزِنُوا۟ بِٱلْقِسْطَاسِ ٱلْمُسْتَقِيمِ

Wa zinoo bilqistaasil mustaqeem

"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."

Aya 183

وَلَا تَبْخَسُوا۟ ٱلنَّاسَ أَشْيَآءَهُمْ وَلَا تَعْثَوْا۟ فِى ٱلْأَرْضِ مُفْسِدِينَ

Wa laa tabkhasun naasa ashyaaa 'ahum wa laa ta'saw fil ardi mufsideen

"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."

Aya 184

وَٱتَّقُوا۟ ٱلَّذِى خَلَقَكُمْ وَٱلْجِبِلَّةَ ٱلْأَوَّلِينَ

Wattaqul lazee khalaqakum waljibillatal awwaleen

"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."

Aya 185

قَالُوٓا۟ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلْمُسَحَّرِينَ

Qaalooo innamaa anta minal musahhareen

Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."

Aya 186

وَمَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٌۭ مِّثْلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ ٱلْكَٰذِبِينَ

Wa maaa anta illaa basharum mislunaa wa innazunnuka laminal kaazibeen

"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."

Aya 187

فَأَسْقِطْ عَلَيْنَا كِسَفًۭا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّٰدِقِينَ

Fa asqit 'alainaa kisafam minas samaaa'i in kunta minas saadiqeen

"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."

Aya 188

قَالَ رَبِّىٓ أَعْلَمُ بِمَا تَعْمَلُونَ

Qaala Rabbeee a'lamu bimaa ta'maloon

Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."

Aya 189

فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمْ عَذَابُ يَوْمِ ٱلظُّلَّةِ ۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍ

Fakazzaboohu fa akhazahum 'azaabu Yawmiz zullah; innahoo kaana 'azaaba Yawmin 'Azeem

Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.

Aya 190

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَءَايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

Inna fee zaalika la Aayah; wa maa kaana aksaruhum mu'mineen

Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Aya 191

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Wa inna Rabbaka la huwal 'Azeezur Raheem

Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Aya 192

وَإِنَّهُۥ لَتَنزِيلُ رَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Wa innahoo latanzeelu Rabbil 'aalameen

Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.

Aya 193

نَزَلَ بِهِ ٱلرُّوحُ ٱلْأَمِينُ

Nazala bihir Roohul Ameen

Rũhi amintacce ne ya sauka da shi.

Aya 194

عَلَىٰ قَلْبِكَ لِتَكُونَ مِنَ ٱلْمُنذِرِينَ

'Alaa qalbika litakoona minal munzireen

A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.

Aya 195

بِلِسَانٍ عَرَبِىٍّۢ مُّبِينٍۢ

Bilisaanin 'Arabiyyim mubeen

Da harshe na Larabci mai bayãni.

Aya 196

وَإِنَّهُۥ لَفِى زُبُرِ ٱلْأَوَّلِينَ

Wa innahoo lafee Zuburil awwaleen

Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.

Aya 197

أَوَلَمْ يَكُن لَّهُمْ ءَايَةً أَن يَعْلَمَهُۥ عُلَمَٰٓؤُا۟ بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ

Awalam yakul lahum Aayatan ai ya'lamahoo 'ulamaaa'u Baneee Israaa'eel

Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?

Aya 198

وَلَوْ نَزَّلْنَٰهُ عَلَىٰ بَعْضِ ٱلْأَعْجَمِينَ

Wa law nazzalnaahu 'alaa ba'dil a'jameen

Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,

Aya 199

فَقَرَأَهُۥ عَلَيْهِم مَّا كَانُوا۟ بِهِۦ مُؤْمِنِينَ

Faqara ahoo 'alaihim maa kaanoo bihee mu'mineen

Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.

Aya 200

كَذَٰلِكَ سَلَكْنَٰهُ فِى قُلُوبِ ٱلْمُجْرِمِينَ

Kazaalika salaknaahu fee quloobil mujrimeen

Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.

Aya 201

لَا يُؤْمِنُونَ بِهِۦ حَتَّىٰ يَرَوُا۟ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَلِيمَ

Laa yu'minoona bihee hattaa yarawul 'azaabal aleem

Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.

Aya 202

فَيَأْتِيَهُم بَغْتَةًۭ وَهُمْ لَا يَشْعُرُونَ

Fayaatiyahum baghtatanw wa hum laa yash'uroon

Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.

Aya 203

فَيَقُولُوا۟ هَلْ نَحْنُ مُنظَرُونَ

Fa yaqooloo hal nahnu munzaroon

Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"

Aya 204

أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ

Aafabi 'azaabinaa yasta'jiloon

Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?

Aya 205

أَفَرَءَيْتَ إِن مَّتَّعْنَٰهُمْ سِنِينَ

Aara'aita im matta'naahum sineen

Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,

Aya 206

ثُمَّ جَآءَهُم مَّا كَانُوا۟ يُوعَدُونَ

Summa jaaa'ahum maa kaanoo yoo'adoon

Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,

Aya 207

مَآ أَغْنَىٰ عَنْهُم مَّا كَانُوا۟ يُمَتَّعُونَ

Maaa aghnaaa 'anhum maa kaanoo yumaatoo'oon

Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su.

Aya 208

وَمَآ أَهْلَكْنَا مِن قَرْيَةٍ إِلَّا لَهَا مُنذِرُونَ

Wa maaa ahlaknaa min qaryatin illaa lahaa munziroon

Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.

Aya 209

ذِكْرَىٰ وَمَا كُنَّا ظَٰلِمِينَ

Zikraa wa maa kunnaa zaalimeen

Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.

Aya 210

وَمَا تَنَزَّلَتْ بِهِ ٱلشَّيَٰطِينُ

Wa maa tanazzalat bihish Shayaateen

Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.

Aya 211

وَمَا يَنۢبَغِى لَهُمْ وَمَا يَسْتَطِيعُونَ

Wa maa yambaghee lahum wa maa yastatee'oon

Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.

Aya 212

إِنَّهُمْ عَنِ ٱلسَّمْعِ لَمَعْزُولُونَ

Innahum 'anis sam'i lama'zooloon

Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.

Aya 213

فَلَا تَدْعُ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ فَتَكُونَ مِنَ ٱلْمُعَذَّبِينَ

Falaa tad'u ma'al laahi ilaahan aakhara fatakoona minal mu'azzabeen

Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.

Aya 214

وَأَنذِرْ عَشِيرَتَكَ ٱلْأَقْرَبِينَ

Wa anzir 'asheeratakal aqrabeen

Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.

Aya 215

وَٱخْفِضْ جَنَاحَكَ لِمَنِ ٱتَّبَعَكَ مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ

Wakhfid janaahaka limanit taba 'aka minal mu'mineen

Kuma ka sassauta fikãfikanka ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.

Aya 216

فَإِنْ عَصَوْكَ فَقُلْ إِنِّى بَرِىٓءٌۭ مِّمَّا تَعْمَلُونَ

Fa in asawka faqul innee bareee'um mimmmaa ta'maloon

Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."

Aya 217

وَتَوَكَّلْ عَلَى ٱلْعَزِيزِ ٱلرَّحِيمِ

Wa tawakkal alal 'Azeezir Raheem

Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Aya 218

ٱلَّذِى يَرَىٰكَ حِينَ تَقُومُ

Allazee yaraaka heena taqoom

Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.

Aya 219

وَتَقَلُّبَكَ فِى ٱلسَّٰجِدِينَ

Wa taqallubaka fis saajideen

Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.

Aya 220

إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلْعَلِيمُ

Innahoo Huwas Samee'ul 'Aleem

Lalle Shi, Shi ne Mai ji, Masani.

Aya 221

هَلْ أُنَبِّئُكُمْ عَلَىٰ مَن تَنَزَّلُ ٱلشَّيَٰطِينُ

Hal unabbi'ukum 'alaa man tanazzalush Shayaateen

Shin, (kunã so) in gaya muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?

Aya 222

تَنَزَّلُ عَلَىٰ كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٍۢ

Tanazzalu 'alaa kulli affaakin aseem

Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.

Aya 223

يُلْقُونَ ٱلسَّمْعَ وَأَكْثَرُهُمْ كَٰذِبُونَ

Yulqoonas sam'a wa aksaruhum aaziboon

Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.

Aya 224

وَٱلشُّعَرَآءُ يَتَّبِعُهُمُ ٱلْغَاوُۥنَ

Washshu 'araaa'u yattabi 'uhumul ghaawoon

Kuma mawãƙa halakakku ne ke bin su.

Aya 225

أَلَمْ تَرَ أَنَّهُمْ فِى كُلِّ وَادٍۢ يَهِيمُونَ

Alam tara annahum fee kulli waadiny yaheemoon

Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?

Aya 226

وَأَنَّهُمْ يَقُولُونَ مَا لَا يَفْعَلُونَ

Wa annahum yaqooloona ma laa yaf'aloon

Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?

Aya 227

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّٰلِحَٰتِ وَذَكَرُوا۟ ٱللَّهَ كَثِيرًۭا وَٱنتَصَرُوا۟ مِنۢ بَعْدِ مَا ظُلِمُوا۟ ۗ وَسَيَعْلَمُ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓا۟ أَىَّ مُنقَلَبٍۢ يَنقَلِبُونَ

Illal lazeena aamanoo w a'amilus saalihaati wa zakarul laaha kaseeranw wantasaroo mim ba'di maa zulimoo; wa saya'lamul lazeena zalamooo aiya munqalbiny yanqaliboon

Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.