Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Zariyat
51

Zariyat — Masu Watsawa

الذَّارِيَاتِ
Makkiyya Aya 60
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَٱلذَّٰرِيَٰتِ ذَرْوًۭا

Waz-zaariyaati zarwaa

Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.

Aya 2

فَٱلْحَٰمِلَٰتِ وِقْرًۭا

Falhaamilaati wiqraa

Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).

Aya 3

فَٱلْجَٰرِيَٰتِ يُسْرًۭا

Faljaariyaati yusraa

Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.

Aya 4

فَٱلْمُقَسِّمَٰتِ أَمْرًا

Falmuqassimaati amraa

Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).

Aya 5

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٌۭ

Innamaa too'adoona la-saadiq

Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.

Aya 6

وَإِنَّ ٱلدِّينَ لَوَٰقِعٌۭ

Wa innad deena la waaqi'

Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne

Aya 7

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلْحُبُكِ

Wassamaaa'i zaatil hubuk

Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).

Aya 8

إِنَّكُمْ لَفِى قَوْلٍۢ مُّخْتَلِفٍۢ

Innakum lafee qawlim mukhtalif

Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).

Aya 9

يُؤْفَكُ عَنْهُ مَنْ أُفِكَ

Yu'faku 'anhu man ufik

Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).

Aya 10

قُتِلَ ٱلْخَرَّٰصُونَ

Qutilal kharraasoon

An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.

Aya 11

ٱلَّذِينَ هُمْ فِى غَمْرَةٍۢ سَاهُونَ

Allazeena hum fee ghamratin saahoon

Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.

Aya 12

يَسْـَٔلُونَ أَيَّانَ يَوْمُ ٱلدِّينِ

Yas'aloona ayyaana yawmud Deen

Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"

Aya 13

يَوْمَ هُمْ عَلَى ٱلنَّارِ يُفْتَنُونَ

Yawma hum 'alan naari yuftanoon

Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.

Aya 14

ذُوقُوا۟ فِتْنَتَكُمْ هَٰذَا ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تَسْتَعْجِلُونَ

Zooqoo fitnatakum haa zal lazee kuntum bihee tas ta'jiloon

(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."

Aya 15

إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّٰتٍۢ وَعُيُونٍ

Innal muttaqeena fee jannaatinw wa 'uyoon

Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.

Aya 16

ءَاخِذِينَ مَآ ءَاتَىٰهُمْ رَبُّهُمْ ۚ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَبْلَ ذَٰلِكَ مُحْسِنِينَ

Aakhizeena maaa aataahum Rabbuhum; innahum kaanoo qabla zaalika muhsineen

Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).

Aya 17

كَانُوا۟ قَلِيلًۭا مِّنَ ٱلَّيْلِ مَا يَهْجَعُونَ

kaanoo qaleelam minal laili maa yahja'oon

Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.

Aya 18

وَبِٱلْأَسْحَارِ هُمْ يَسْتَغْفِرُونَ

Wa bilashaari hum yastaghfiroon

Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.

Aya 19

وَفِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّۭ لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ

Wa feee amwaalihim haqqul lissaaa'ili walmahroom

Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.

Aya 20

وَفِى ٱلْأَرْضِ ءَايَٰتٌۭ لِّلْمُوقِنِينَ

Wa fil ardi aayaatul lilmooqineen

Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.

Aya 21

وَفِىٓ أَنفُسِكُمْ ۚ أَفَلَا تُبْصِرُونَ

Wa feee anfusikum; afalaa tubsiroon

Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?

Aya 22

وَفِى ٱلسَّمَآءِ رِزْقُكُمْ وَمَا تُوعَدُونَ

Wa fissamaaa'i rizqukum wa maa too'adoon

Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.

Aya 23

فَوَرَبِّ ٱلسَّمَآءِ وَٱلْأَرْضِ إِنَّهُۥ لَحَقٌّۭ مِّثْلَ مَآ أَنَّكُمْ تَنطِقُونَ

Fawa Rabbis samaaa'i wal ardi innahoo lahaqqum misla maa annakum tantiqoon

To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,

Aya 24

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ضَيْفِ إِبْرَٰهِيمَ ٱلْمُكْرَمِينَ

Hal ataaka hadeesu daifi Ibraaheemal mukrameen

Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?

Aya 25

إِذْ دَخَلُوا۟ عَلَيْهِ فَقَالُوا۟ سَلَٰمًۭا ۖ قَالَ سَلَٰمٌۭ قَوْمٌۭ مُّنكَرُونَ

Iz dakhaloo 'alaihi faqaaloo salaaman qaala salaamun qawmum munkaroon

A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"

Aya 26

فَرَاغَ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ فَجَآءَ بِعِجْلٍۢ سَمِينٍۢ

Faraagha ilaaa ahlihee fajaaa'a bi'ijlin sameen

Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,

Aya 27

فَقَرَّبَهُۥٓ إِلَيْهِمْ قَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ

Faqarrabahooo ilaihim qaala alaa taakuloon

Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"

Aya 28

فَأَوْجَسَ مِنْهُمْ خِيفَةًۭ ۖ قَالُوا۟ لَا تَخَفْ ۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَٰمٍ عَلِيمٍۢ

Fa awjasa minhm khee fatan qaaloo laa takhaf wa bashsharoohu bighulaamin 'aleem

Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.

Aya 29

فَأَقْبَلَتِ ٱمْرَأَتُهُۥ فِى صَرَّةٍۢ فَصَكَّتْ وَجْهَهَا وَقَالَتْ عَجُوزٌ عَقِيمٌۭ

Fa aqbalatim ra-atuhoo fee sarratin fasakkat wajhahaa wa qaalat 'ajoozun 'aqeem

Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"

Aya 30

قَالُوا۟ كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِ ۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلْحَكِيمُ ٱلْعَلِيمُ

Qaaloo kazaaliki qaala Rabbuki innahoo huwal hakeemul 'aleem

Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."

Aya 31

۞ قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا ٱلْمُرْسَلُونَ

Qaala famaa khatbukum ayyuhal mursaloon

(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"

Aya 32

قَالُوٓا۟ إِنَّآ أُرْسِلْنَآ إِلَىٰ قَوْمٍۢ مُّجْرِمِينَ

Qaalooo innaaa ursilnaaa ilaa qawmim mujrimeen

Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.

Aya 33

لِنُرْسِلَ عَلَيْهِمْ حِجَارَةًۭ مِّن طِينٍۢ

Linursila 'alaihim hijaa ratam min teen

"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).

Aya 34

مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلْمُسْرِفِينَ

Musawwamatan 'inda rabbika lilmusrifeen

"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."

Aya 35

فَأَخْرَجْنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ

Fa akhrajnaa man kaana feehaa minal mu'mineen

Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.

Aya 36

فَمَا وَجَدْنَا فِيهَا غَيْرَ بَيْتٍۢ مِّنَ ٱلْمُسْلِمِينَ

Famaa wajadnaa feehaa ghaira baitim minal muslimeen

Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.

Aya 37

وَتَرَكْنَا فِيهَآ ءَايَةًۭ لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَلِيمَ

Wa taraknaa feehaaa aayatal lillazeena yakhaafoonal 'azaabal aleem

Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.

Aya 38

وَفِى مُوسَىٰٓ إِذْ أَرْسَلْنَٰهُ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ بِسُلْطَٰنٍۢ مُّبِينٍۢ

Wa fee Moosaaa iz arsalnaahu ilaa Fir'wna bisultaa nim mubeen

Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.

Aya 39

فَتَوَلَّىٰ بِرُكْنِهِۦ وَقَالَ سَٰحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌۭ

Fatawalla biruknihee wa qaala saahirun aw majnoon

Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"

Aya 40

فَأَخَذْنَٰهُ وَجُنُودَهُۥ فَنَبَذْنَٰهُمْ فِى ٱلْيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٌۭ

Fa akhaznaahu wa junoo dahoo fanabaznaahum fil yammi wa huwa muleem

Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

Aya 41

وَفِى عَادٍ إِذْ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمُ ٱلرِّيحَ ٱلْعَقِيمَ

Wa fee 'Aadin iz arsalnaa 'alaihimur reehal'aqeem

Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.

Aya 42

مَا تَذَرُ مِن شَىْءٍ أَتَتْ عَلَيْهِ إِلَّا جَعَلَتْهُ كَٱلرَّمِيمِ

Maa tazaru min shai'in atat 'alaihi illaa ja'alat hu karrameem

Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.

Aya 43

وَفِى ثَمُودَ إِذْ قِيلَ لَهُمْ تَمَتَّعُوا۟ حَتَّىٰ حِينٍۢ

Wa fee Samooda iz qeela lahum tamatta''oo hattaa heen

Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"

Aya 44

فَعَتَوْا۟ عَنْ أَمْرِ رَبِّهِمْ فَأَخَذَتْهُمُ ٱلصَّٰعِقَةُ وَهُمْ يَنظُرُونَ

Fa'ataw 'an amri Rabbihim fa akhazal humus saa'iqatu wa hum yanzuroon

Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.

Aya 45

فَمَا ٱسْتَطَٰعُوا۟ مِن قِيَامٍۢ وَمَا كَانُوا۟ مُنتَصِرِينَ

Famas tataa'oo min qiyaaminw wa maa kaanoo muntasireen

Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.

Aya 46

وَقَوْمَ نُوحٍۢ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَوْمًۭا فَٰسِقِينَ

Wa qawma Noohim min qablu innahum kaano qawman faasiqeen

Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.

Aya 47

وَٱلسَّمَآءَ بَنَيْنَٰهَا بِأَيْي۟دٍۢ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ

Wassamaaa'a banainaa haa bi aydinw wa innaa lamoosi'oon

Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.

Aya 48

وَٱلْأَرْضَ فَرَشْنَٰهَا فَنِعْمَ ٱلْمَٰهِدُونَ

Wal arda farashnaahaa fani'mal maahidoon

Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,

Aya 49

وَمِن كُلِّ شَىْءٍ خَلَقْنَا زَوْجَيْنِ لَعَلَّكُمْ تَذَكَّرُونَ

Wa min kulli shai'in khalaqnaa zawjaini la'allakum tazakkaroon

Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.

Aya 50

فَفِرُّوٓا۟ إِلَى ٱللَّهِ ۖ إِنِّى لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌۭ مُّبِينٌۭ

Fafirrooo ilal laahi innee lakum minhu nazeerum mubeen

Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

Aya 51

وَلَا تَجْعَلُوا۟ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ ۖ إِنِّى لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌۭ مُّبِينٌۭ

Wa laa taj'aloo ma'al laahi ilaahan aakhara innee lakum minhu nazeerum mubeen

Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

Aya 52

كَذَٰلِكَ مَآ أَتَى ٱلَّذِينَ مِن قَبْلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا قَالُوا۟ سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ

Kazaalika maaa atal lazeena min qablihim mir Rasoolin illaa qaaloo saahirun aw majnoon

Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."

Aya 53

أَتَوَاصَوْا۟ بِهِۦ ۚ بَلْ هُمْ قَوْمٌۭ طَاغُونَ

Atawaasaw bih; bal hum qawmun taaghoon

shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.

Aya 54

فَتَوَلَّ عَنْهُمْ فَمَآ أَنتَ بِمَلُومٍۢ

Fatawalla 'anhum famaaa anta bimaloom

Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.

Aya 55

وَذَكِّرْ فَإِنَّ ٱلذِّكْرَىٰ تَنفَعُ ٱلْمُؤْمِنِينَ

Wa zakkir fa innaz zikraa tanfa'ul mu'mineen

Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.

Aya 56

وَمَا خَلَقْتُ ٱلْجِنَّ وَٱلْإِنسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ

Wa maa khalaqtul jinna wal insa illaa liya'budoon

Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.

Aya 57

مَآ أُرِيدُ مِنْهُم مِّن رِّزْقٍۢ وَمَآ أُرِيدُ أَن يُطْعِمُونِ

Maaa ureedu minhum mir rizqinw wa maaa ureedu anyyut'imoon

Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.

Aya 58

إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلرَّزَّاقُ ذُو ٱلْقُوَّةِ ٱلْمَتِينُ

Innal laaha Huwar Razzaaqu Zul Quwwatil Mateen

Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.

Aya 59

فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ ذَنُوبًۭا مِّثْلَ ذَنُوبِ أَصْحَٰبِهِمْ فَلَا يَسْتَعْجِلُونِ

Fa inna lillazeena zalamoo zanoobam misla zanoobi ashaabihim falaa yasta'jiloon

To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.

Aya 60

فَوَيْلٌۭ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا۟ مِن يَوْمِهِمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ

Fawailul lillazeena kafaroo miny yawmihimul lazee yoo'adoon

Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.