Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Ɗur
52

Ɗur — Dutse

الطُّورِ
Makkiyya Aya 49
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَٱلطُّورِ

Wat-Toor

Inã rantsuwa da ¦ũr (Dũtsen Mũsã).

Aya 2

وَكِتَٰبٍۢ مَّسْطُورٍۢ

Wa kitaabim mastoor

Da wani littãfi rubũtacce.

Aya 3

فِى رَقٍّۢ مَّنشُورٍۢ

Fee raqqim manshoor

A cikin wata takardar fãta shimfiɗaɗɗa.

Aya 4

وَٱلْبَيْتِ ٱلْمَعْمُورِ

Wal baitil ma'moor

Da Gidan da aka rãyar da shi (da ibãda).

Aya 5

وَٱلسَّقْفِ ٱلْمَرْفُوعِ

Wassaqfil marfoo'

Da rufin nan da aka ɗaukaka.

Aya 6

وَٱلْبَحْرِ ٱلْمَسْجُورِ

Wal bahril masjoor

Da tẽkun nan da aka cika (da ruwa).

Aya 7

إِنَّ عَذَابَ رَبِّكَ لَوَٰقِعٌۭ

Inna 'azaaba Rabbika lawaaqi'

Lalle, azãbar Ubangijinka, haƙĩƙa, mai aukuwa ce.

Aya 8

مَّا لَهُۥ مِن دَافِعٍۢ

Maa lahoo min daafi'

Bã ta da mai tunkuɗẽwa.

Aya 9

يَوْمَ تَمُورُ ٱلسَّمَآءُ مَوْرًۭا

Yawma tamoorus samaaa'u mawraa

Rãnar da samã ke yin mõtsi tanã kai kãwo.

Aya 10

وَتَسِيرُ ٱلْجِبَالُ سَيْرًۭا

Wa taseerul jibaalu sairaa

Kuma duwãtsu nã tafiya sunã shũɗẽwa.

Aya 11

فَوَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Fawailuny yawma 'izil lil mukaazzibeen

To, bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.

Aya 12

ٱلَّذِينَ هُمْ فِى خَوْضٍۢ يَلْعَبُونَ

Allazeena hum fee khawdiny yal'aboon

Waɗanda suke a cikin kududdufi sunã wãsã.

Aya 13

يَوْمَ يُدَعُّونَ إِلَىٰ نَارِ جَهَنَّمَ دَعًّا

Yawma yuda'-'oona ilaa naari jahannama da'-'aa

Rãnar da zã a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗãwa.

Aya 14

هَٰذِهِ ٱلنَّارُ ٱلَّتِى كُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَ

Haazihin naarul latee kuntum bihaa tukazziboon

(A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."

Aya 15

أَفَسِحْرٌ هَٰذَآ أَمْ أَنتُمْ لَا تُبْصِرُونَ

Afasihrun haazaaaa am antum laa tubsiroon

"To, shin wannan sihiri ne kõ kuwa kũ ne bã ku gani?"

Aya 16

ٱصْلَوْهَا فَٱصْبِرُوٓا۟ أَوْ لَا تَصْبِرُوا۟ سَوَآءٌ عَلَيْكُمْ ۖ إِنَّمَا تُجْزَوْنَ مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ

Islawhaa fasbirooo aw laa tasbiroo sawaaa'un 'alaikum innamaa tujzawna maa kuntum ta'maloon

"Ku shigẽ ta. To, ku yi haƙuri ko kuma kada ku yi haƙuri, dai dai ne a kanku, kawai anã yi muku sakamakon abin da kuka kasance kunã aikatãwa."

Aya 17

إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّٰتٍۢ وَنَعِيمٍۢ

Innal muttaqeena fee jannaatinw wa na'eem

Lalle, mãsu taƙawa, sunã a cikin gidãjen Aljanna da wata ni'ima.

Aya 18

فَٰكِهِينَ بِمَآ ءَاتَىٰهُمْ رَبُّهُمْ وَوَقَىٰهُمْ رَبُّهُمْ عَذَابَ ٱلْجَحِيمِ

Faakiheena bimaaa aataahum rabbuhum wa waqaahum rabbuhum 'azaabal jaheem

Sunã mãsu jin dãɗi da abin da Ubangijinsu Ya ba su, kuma Ubangijinsu Ya tsãre musu azãbar Jahĩm.

Aya 19

كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ

Kuloo washraboo haneee 'am bimaa kuntum ta'maloon

(A ce musu): "Ku ci, ku sha, da ni'ima, dõmin abin da kuka kasance kunã aikatãwa."

Aya 20

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ سُرُرٍۢ مَّصْفُوفَةٍۢ ۖ وَزَوَّجْنَٰهُم بِحُورٍ عِينٍۢ

Muttaki'eena 'alaa sururim masfoofatinw wa zawwaj naahum bihoorin 'een

Sunã kishingiɗe a kan karagu waɗanda ke cikin sahu, kuma Muka aurar da su waɗansu mãtã mãsu farin idãnu, mãsu girmansu.

Aya 21

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَٱتَّبَعَتْهُمْ ذُرِّيَّتُهُم بِإِيمَٰنٍ أَلْحَقْنَا بِهِمْ ذُرِّيَّتَهُمْ وَمَآ أَلَتْنَٰهُم مِّنْ عَمَلِهِم مِّن شَىْءٍۢ ۚ كُلُّ ٱمْرِئٍۭ بِمَا كَسَبَ رَهِينٌۭ

Wallazeena aamanoo wattaba'at hum zurriyyatuhum bieemaanin alhaqnaa bihim zurriyyatahum wa maaa alatnaahum min 'amalihim min shai'; kullum ri'im bimaa kasaba raheen

Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma zũriyarsu suka bĩ su ga ĩmãnin, Mun riskar da zũriyarsu da su, alhãli kuwa bã da Mun rage musu kõme ba daga aikinsu, kõwane mutum jingina ne ga abin da ya sana'anta.

Aya 22

وَأَمْدَدْنَٰهُم بِفَٰكِهَةٍۢ وَلَحْمٍۢ مِّمَّا يَشْتَهُونَ

Wa amdadnaahum bifaa kihatinw wa lahmim mimmaa yashtahoon

Kuma Muka yalwata musu 'ya'yan itãce da nãma irin wanda suke marmari.

Aya 23

يَتَنَٰزَعُونَ فِيهَا كَأْسًۭا لَّا لَغْوٌۭ فِيهَا وَلَا تَأْثِيمٌۭ

Yatanaaza'oona feehaa kaasal laa laghwun feehaa wa laa taaseem

Sunã mĩƙa wa jũnansu a cikinta hinjãlan giya, wadda bãbu yãsassar magana a cikinta, kuma bãbu jin nauyin zunubi.

Aya 24

۞ وَيَطُوفُ عَلَيْهِمْ غِلْمَانٌۭ لَّهُمْ كَأَنَّهُمْ لُؤْلُؤٌۭ مَّكْنُونٌۭ

Wa yatoofu 'alaihim ghilmaanul lahum ka annahum lu'lu'um maknoon

Kuma waɗansu samãri nã gẽwayãwa a kansu, kamar dai sũ lu'ulu'u ne wanda ke kulle.

Aya 25

وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَسَآءَلُونَ

Wa aqbala ba'duhum 'alaa ba'diny yatasaaa'aloon

Waɗansunsu suka fuskanta zuwa ga waɗansu, sunã tambayar jũna.

Aya 26

قَالُوٓا۟ إِنَّا كُنَّا قَبْلُ فِىٓ أَهْلِنَا مُشْفِقِينَ

Qaalooo innaa kunnaa qablu feee ahlinaa mushfiqeen

Suka ce: "Lalle mũ mun kasance a gabãnin wannan (a dũniya) a cikin iyãlanmu munã jin tsõro."

Aya 27

فَمَنَّ ٱللَّهُ عَلَيْنَا وَوَقَىٰنَا عَذَابَ ٱلسَّمُومِ

Famannnal laahu 'alainaa wa waqaanaa 'azaabas samoom

"To, Allah Yã yi mana kyautar falala, kuma Yã tsare mana azãbar iskar zãfi."

Aya 28

إِنَّا كُنَّا مِن قَبْلُ نَدْعُوهُ ۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلْبَرُّ ٱلرَّحِيمُ

Innaa kunnaa min qablu nad'oohu innahoo huwal barrur raheem

"Lalle mũ mun kasance, a gãbanin haka, munã kiran sa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai kyautatãwa, Mai rahama."

Aya 29

فَذَكِّرْ فَمَآ أَنتَ بِنِعْمَتِ رَبِّكَ بِكَاهِنٍۢ وَلَا مَجْنُونٍ

Fazakkir famaaa anta bini'mati rabbika bikaahininw wa laa majnoon

To, ka tunãtar kai fa sabõda ni'imar Ubangjinka, bã bõka kake ba, kuma bã mahaukaci ba.

Aya 30

أَمْ يَقُولُونَ شَاعِرٌۭ نَّتَرَبَّصُ بِهِۦ رَيْبَ ٱلْمَنُونِ

Am yaqooloona shaa'irun natarabbasu bihee raibal manoon

Shin zã su ce: "Mawãƙi ne, munã jiran, masĩfun mutuwa game da shĩ"?

Aya 31

قُلْ تَرَبَّصُوا۟ فَإِنِّى مَعَكُم مِّنَ ٱلْمُتَرَبِّصِينَ

Qul tarabbasoo fa innee ma'akum minal mutarabbiseen

Ka ce: "Ku yi jira, domin nĩ ma lalle inã a cikin mãsu jira tãre da ku."

Aya 32

أَمْ تَأْمُرُهُمْ أَحْلَٰمُهُم بِهَٰذَآ ۚ أَمْ هُمْ قَوْمٌۭ طَاغُونَ

Am taamuruhum ahlaamuhum bihaazaaa am hum qawmun taaghoon

Shin, hankulansu ne ke umarin su da wannan, kõ kuwa sũ wasu mutãne ne mãsu ƙetare haddi?

Aya 33

أَمْ يَقُولُونَ تَقَوَّلَهُۥ ۚ بَل لَّا يُؤْمِنُونَ

Am yaqooloona taqawwalah; bal laa yu'minoon

Shin, cẽwa suke yi: "Shi ne ke ƙãga faɗarsa"? Ã'a ba su dai yi ĩmãni ba.

Aya 34

فَلْيَأْتُوا۟ بِحَدِيثٍۢ مِّثْلِهِۦٓ إِن كَانُوا۟ صَٰدِقِينَ

Falyaatoo bihadeesim misliheee in kaanoo saadiqeen

Sai su zõ da wani lãbãri mai misãlinsa idan sun kasance sũmãsu gaskiya ne.

Aya 35

أَمْ خُلِقُوا۟ مِنْ غَيْرِ شَىْءٍ أَمْ هُمُ ٱلْخَٰلِقُونَ

Am khuliqoo min ghairi shai'in am humul khaaliqoon

Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta?

Aya 36

أَمْ خَلَقُوا۟ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضَ ۚ بَل لَّا يُوقِنُونَ

Am khalaqus samaawaati wal ard; bal laa yooqinoon

Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba.

Aya 37

أَمْ عِندَهُمْ خَزَآئِنُ رَبِّكَ أَمْ هُمُ ٱلْمُصَۣيْطِرُونَ

Am'indahum khazaaa'inu rabbika am humul musaitiroon

Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya?

Aya 38

أَمْ لَهُمْ سُلَّمٌۭ يَسْتَمِعُونَ فِيهِ ۖ فَلْيَأْتِ مُسْتَمِعُهُم بِسُلْطَٰنٍۢ مُّبِينٍ

Am lahum sullamuny yastami'oona feehi falyaati mustami'uhum bisultaanim mubeen

Shin, sunã da wani tsãni ne wanda suke (hawa sunã) saurãron (lãbãrin samã) a cikinsa? Sai mai saurarõnsu ya zo da wani dalĩli bayyananne.

Aya 39

أَمْ لَهُ ٱلْبَنَٰتُ وَلَكُمُ ٱلْبَنُونَ

Am lahul banaatu wa lakumul banoon

Shin, Yanã da 'ya'ya mãtã ne kuma kũ, kunã da ɗiya maza ne?

Aya 40

أَمْ تَسْـَٔلُهُمْ أَجْرًۭا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍۢ مُّثْقَلُونَ

Am tas'aluhum ajran fahum mim maghramim musqaloon

Shin, kanã tambayar su wata ijãra ne, sabõda haka suka zama mãsu jin nauyin biyan tãrar?

Aya 41

أَمْ عِندَهُمُ ٱلْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ

Am 'indahumul ghaibu fahum yaktuboon

Shin, a wurinsu akwai ilmin gaibi, sabõda haka sunã rubũtãwa?

Aya 42

أَمْ يُرِيدُونَ كَيْدًۭا ۖ فَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ هُمُ ٱلْمَكِيدُونَ

Am yureedoona kaidan fallazeena kafaroo humul makeedoon

Shin, sunã nufin wani kaidi ne? To, waɗanda suka kãfirta sũ ne waɗanda ake yi wa kaidi.

Aya 43

أَمْ لَهُمْ إِلَٰهٌ غَيْرُ ٱللَّهِ ۚ سُبْحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يُشْرِكُونَ

Am lahum ilaahun ghairul laa; subhaanal laahi 'ammaa yushrikoon

Shin, sunã da wani abin bautãwa ne wanda bã Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke yi na shirki!

Aya 44

وَإِن يَرَوْا۟ كِسْفًۭا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ سَاقِطًۭا يَقُولُوا۟ سَحَابٌۭ مَّرْكُومٌۭ

Wa iny yaraw kisfam minas samaaa'i saaqitany yaqooloo sahaabum markoom

Kuma idan sun ga wani ɓaɓɓake daga samã yãnã fãɗuwa, sai su ce wani girgije ne, mai hauhawar jũna.

Aya 45

فَذَرْهُمْ حَتَّىٰ يُلَٰقُوا۟ يَوْمَهُمُ ٱلَّذِى فِيهِ يُصْعَقُونَ

Fazarhum hatta yulaaqoo yawmahumul lazee feehi yus'aqoon

To, ka bar su, sai sun haɗu da yinin nan da za a sũmar da su a cikinsa.

Aya 46

يَوْمَ لَا يُغْنِى عَنْهُمْ كَيْدُهُمْ شَيْـًۭٔا وَلَا هُمْ يُنصَرُونَ

Yawma laa yughnee 'anhum kaidumhum shai'anw wa laa hum yunsaroon

Rãnar da kaidinsu bã ya wadãtar masu da kõme, kuma bã a taimakon su.

Aya 47

وَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ عَذَابًۭا دُونَ ذَٰلِكَ وَلَٰكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُونَ

Wa inna lillazeena zalamoo 'azaaban doona zalika wa laakinna aksarahum laa ya'lamoon

Kuma lalle, waɗannan da suka yi zãluncin, sunã da azãba (a nan dũniya) banda waccan, kuma mafi yawansu ba su sani ba.

Aya 48

وَٱصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ فَإِنَّكَ بِأَعْيُنِنَا ۖ وَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ حِينَ تَقُومُ

Wasbir lihukmi rabbika fa innaka bi-a'yuninaa wa sabbih bihamdi rabbika heena taqoom

Sai ka yi hakuri da hukuncin Ubangijinka, lalle kai fa kanã idãnunMu, kuma ka tsarkake Ubangijinka da (tasbĩhi) game da gõde Masa a lõkacin da kake tãshi tsaye (dõmin salla kõ wani abu).

Aya 49

وَمِنَ ٱلَّيْلِ فَسَبِّحْهُ وَإِدْبَٰرَ ٱلنُّجُومِ

Wa minal laili fasabbihhu wa idbaaran nujoom

Kuma daga dare, sai ka tsarkake Shi (da tasbĩhin) dalõkacin jũyãwar taurãri.