Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Najm
53

Najm — Tauraro

النَّجۡمِ
Makkiyya Aya 62
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَٱلنَّجْمِ إِذَا هَوَىٰ

Wannajmi izaa hawaa

Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.

Aya 2

مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمْ وَمَا غَوَىٰ

Maa dalla saahibukum wa maa ghawaa

Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.

Aya 3

وَمَا يَنطِقُ عَنِ ٱلْهَوَىٰٓ

Wa maa yyantiqu 'anilhawaaa

Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.

Aya 4

إِنْ هُوَ إِلَّا وَحْىٌۭ يُوحَىٰ

In huwa illaa Wahyuny yoohaa

(Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.

Aya 5

عَلَّمَهُۥ شَدِيدُ ٱلْقُوَىٰ

'Allamahoo shadeedul quwaa

(Malã'ika) mai tsananin ƙarfi ya sanar da shi.

Aya 6

ذُو مِرَّةٍۢ فَٱسْتَوَىٰ

Zoo mirratin fastawaa

Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.

Aya 7

وَهُوَ بِٱلْأُفُقِ ٱلْأَعْلَىٰ

Wa huwa bil ufuqil a'laa

Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.

Aya 8

ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىٰ

Summa danaa fatadalla

Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.

Aya 9

فَكَانَ قَابَ قَوْسَيْنِ أَوْ أَدْنَىٰ

Fakaana qaaba qawsaini aw adnaa

Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.

Aya 10

فَأَوْحَىٰٓ إِلَىٰ عَبْدِهِۦ مَآ أَوْحَىٰ

Fa awhaaa ilaa 'abdihee maaa awhaa

Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).

Aya 11

مَا كَذَبَ ٱلْفُؤَادُ مَا رَأَىٰٓ

Maa kazabal fu'aadu maa ra aa

Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.

Aya 12

أَفَتُمَٰرُونَهُۥ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ

Afatumaaroonahoo 'alaa maayaraa

Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?

Aya 13

وَلَقَدْ رَءَاهُ نَزْلَةً أُخْرَىٰ

Wa laqad ra aahu nazlatan ukhraa

Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.

Aya 14

عِندَ سِدْرَةِ ٱلْمُنتَهَىٰ

'Inda sidratil muntaha

A wurin da magaryar tuƙẽwa take.

Aya 15

عِندَهَا جَنَّةُ ٱلْمَأْوَىٰٓ

'Indahaa jannatul maawaa

A inda taken, nan Aljannar makoma take.

Aya 16

إِذْ يَغْشَى ٱلسِّدْرَةَ مَا يَغْشَىٰ

Iz yaghshas sidrata maa yaghshaa

Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.

Aya 17

مَا زَاغَ ٱلْبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ

Maa zaaghal basaru wa maa taghaa

Ganinsa bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.

Aya 18

لَقَدْ رَأَىٰ مِنْ ءَايَٰتِ رَبِّهِ ٱلْكُبْرَىٰٓ

Laqad ra aa min aayaati Rabbihil kubraaa

Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma daga ãyõyin Ubangijinsa.

Aya 19

أَفَرَءَيْتُمُ ٱللَّٰتَ وَٱلْعُزَّىٰ

Afara'aytumul laata wal 'uzzaa

Shin, kun ga Lãta da uzza?

Aya 20

وَمَنَوٰةَ ٱلثَّالِثَةَ ٱلْأُخْرَىٰٓ

Wa manaatas saalisatal ukhraa

Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?

Aya 21

أَلَكُمُ ٱلذَّكَرُ وَلَهُ ٱلْأُنثَىٰ

A-lakumuz zakaru wa lahul unsaa

Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?

Aya 22

تِلْكَ إِذًۭا قِسْمَةٌۭ ضِيزَىٰٓ

Tilka izan qismatun deezaa

Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe.

Aya 23

إِنْ هِىَ إِلَّآ أَسْمَآءٌۭ سَمَّيْتُمُوهَآ أَنتُمْ وَءَابَآؤُكُم مَّآ أَنزَلَ ٱللَّهُ بِهَا مِن سُلْطَٰنٍ ۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ وَمَا تَهْوَى ٱلْأَنفُسُ ۖ وَلَقَدْ جَآءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ ٱلْهُدَىٰٓ

In hiya illaaa asmaaa'un sammaitumoohaaa antum wa aabaaa'ukum maaa anzalal laahu bihaa min sultaan; inyyattabi'oona illaz zanna wa maa tahwal anfusu wa laqad jaaa'ahum mir Rabbihimul hudaa

Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).

Aya 24

أَمْ لِلْإِنسَٰنِ مَا تَمَنَّىٰ

Am lil insaani maa taman naa

Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?

Aya 25

فَلِلَّهِ ٱلْءَاخِرَةُ وَٱلْأُولَىٰ

Falillaahil aakhiratu wal oolaa

To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).

Aya 26

۞ وَكَم مِّن مَّلَكٍۢ فِى ٱلسَّمَٰوَٰتِ لَا تُغْنِى شَفَٰعَتُهُمْ شَيْـًٔا إِلَّا مِنۢ بَعْدِ أَن يَأْذَنَ ٱللَّهُ لِمَن يَشَآءُ وَيَرْضَىٰٓ

Wa kam mim malakin fissamaawaati laa tughnee shafaa'atuhum shai'an illaa mim ba'di anyyaazanal laahu limany yashaaa'u wa yardaa

Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.

Aya 27

إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِٱلْءَاخِرَةِ لَيُسَمُّونَ ٱلْمَلَٰٓئِكَةَ تَسْمِيَةَ ٱلْأُنثَىٰ

innal lazeena laa yu'minoona bil aakhirati la yusammoonal malaaa'ikata tasmiyatal unsaa

Lalle waɗannan da bã su yin ĩmãni da Lãhira, haƙĩƙa sunã kiran malã'iku da sũnan mace.

Aya 28

وَمَا لَهُم بِهِۦ مِنْ عِلْمٍ ۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ ۖ وَإِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغْنِى مِنَ ٱلْحَقِّ شَيْـًۭٔا

Wa maa lahum bihee min 'ilmin iny yattabi'oona illaz zanna wa innaz zanna laa yughnee minal haqqi shai'aa

Kuma bã su da wani ilmi game da shi, bã su bin kõme fãce zato alhãli kuwa lalle zato bã ya amfãnar da kõme daga gaskiya.

Aya 29

فَأَعْرِضْ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكْرِنَا وَلَمْ يُرِدْ إِلَّا ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا

Fa a'rid 'am man tawallaa 'an zikrinaa wa lam yurid illal hayaatad dunyaa

Sabõda haka sai ka kau da kai daga wanda ya jũya bãya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kõme ba fãce rãyuwar kusa (dũniya).

Aya 30

ذَٰلِكَ مَبْلَغُهُم مِّنَ ٱلْعِلْمِ ۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ ٱهْتَدَىٰ

Zalika mablaghuhum minal 'ilm; inna rabbaka huwa a'lamu biman dalla 'an sabee lihee wa huwa a'lamu bimanih tadaa

Wannan ita ce iyãkar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shĩ ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nẽmi shiriya.

Aya 31

وَلِلَّهِ مَا فِى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِى ٱلْأَرْضِ لِيَجْزِىَ ٱلَّذِينَ أَسَٰٓـُٔوا۟ بِمَا عَمِلُوا۟ وَيَجْزِىَ ٱلَّذِينَ أَحْسَنُوا۟ بِٱلْحُسْنَى

Wa lillaahi maa fis samaawaati wa maa fil ardi liyajziyal lazeena asaaa'oo bimaa 'amiloo wa yajziyal lazeena ahsanoo bilhusnaa

Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.

Aya 32

ٱلَّذِينَ يَجْتَنِبُونَ كَبَٰٓئِرَ ٱلْإِثْمِ وَٱلْفَوَٰحِشَ إِلَّا ٱللَّمَمَ ۚ إِنَّ رَبَّكَ وَٰسِعُ ٱلْمَغْفِرَةِ ۚ هُوَ أَعْلَمُ بِكُمْ إِذْ أَنشَأَكُم مِّنَ ٱلْأَرْضِ وَإِذْ أَنتُمْ أَجِنَّةٌۭ فِى بُطُونِ أُمَّهَٰتِكُمْ ۖ فَلَا تُزَكُّوٓا۟ أَنفُسَكُمْ ۖ هُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ ٱتَّقَىٰٓ

Allazeena yajtaniboona kabaaa'iral ismi walfawaa hisha illal lamam; inna rabbaka waasi'ul maghfirah; huwa a'lamu bikum iz ansha akum minal ardi wa iz antum ajinnatun fee butooni umma haatikum falaa tuzakkooo anfusakum huwa a'lamu bimanit taqaa

Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.

Aya 33

أَفَرَءَيْتَ ٱلَّذِى تَوَلَّىٰ

Afara'ayatal lazee tawallaa

Shin, ka ga wannan da ya jũya baya?

Aya 34

وَأَعْطَىٰ قَلِيلًۭا وَأَكْدَىٰٓ

Wa a'taa qaleelanw wa akdaa

Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa?

Aya 35

أَعِندَهُۥ عِلْمُ ٱلْغَيْبِ فَهُوَ يَرَىٰٓ

A'indahoo 'ilmul ghaibi fahuwa yaraa

Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?

Aya 36

أَمْ لَمْ يُنَبَّأْ بِمَا فِى صُحُفِ مُوسَىٰ

Am lam yunabbaa bimaa fee suhuhfi Moosa

Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã?

Aya 37

وَإِبْرَٰهِيمَ ٱلَّذِى وَفَّىٰٓ

Wa Ibraaheemal lazee waffaaa

Da Ibrãhĩm wanda ya cika alkawari?

Aya 38

أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٌۭ وِزْرَ أُخْرَىٰ

Allaa taziru waaziratunw wizra ukhraa

Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.

Aya 39

وَأَن لَّيْسَ لِلْإِنسَٰنِ إِلَّا مَا سَعَىٰ

Wa al laisa lil insaani illaa maa sa'aa

Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.

Aya 40

وَأَنَّ سَعْيَهُۥ سَوْفَ يُرَىٰ

Wa anna sa'yahoo sawfa yuraa

Kuma lalle, aikinsa zã a gan shi.

Aya 41

ثُمَّ يُجْزَىٰهُ ٱلْجَزَآءَ ٱلْأَوْفَىٰ

Summa yujzaahul jazaaa 'al awfaa

Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?

Aya 42

وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلْمُنتَهَىٰ

Wa anna ilaa rabbikal muntahaa

Kuma lalle, makõmar zuwa Ubangijinka kawai take?

Aya 43

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَضْحَكَ وَأَبْكَىٰ

Wa annahoo huwa adhaka wa abkaa

Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.

Aya 44

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَمَاتَ وَأَحْيَا

Wa annahoo huwa amaata wa ahyaa

Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.

Aya 45

وَأَنَّهُۥ خَلَقَ ٱلزَّوْجَيْنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰ

Wa annahoo khalaqaz zawjainiz zakara wal unsaa

Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.

Aya 46

مِن نُّطْفَةٍ إِذَا تُمْنَىٰ

Min nutfatin izaa tumnaa

Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.

Aya 47

وَأَنَّ عَلَيْهِ ٱلنَّشْأَةَ ٱلْأُخْرَىٰ

Wa anna 'alaihin nash atal ukhraa

Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.

Aya 48

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَغْنَىٰ وَأَقْنَىٰ

Wa annahoo huwa aghnaa wa aqnaa

Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.

Aya 49

وَأَنَّهُۥ هُوَ رَبُّ ٱلشِّعْرَىٰ

Wa annahoo huwa rabbush shi'raa

Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.

Aya 50

وَأَنَّهُۥٓ أَهْلَكَ عَادًا ٱلْأُولَىٰ

Wa annahooo ahlak a 'Aadanil oolaa

Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.

Aya 51

وَثَمُودَا۟ فَمَآ أَبْقَىٰ

Wa samooda famaaa abqaa

Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.

Aya 52

وَقَوْمَ نُوحٍۢ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ هُمْ أَظْلَمَ وَأَطْغَىٰ

Wa qawma Noohim min qablu innahum kaanoo hum azlama wa atghaa

Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.

Aya 53

وَٱلْمُؤْتَفِكَةَ أَهْوَىٰ

Wal mu'tafikata ahwaa

Da waɗanda aka birkice ƙasarsu, Ya kãyar da su.

Aya 54

فَغَشَّىٰهَا مَا غَشَّىٰ

Faghashshaahaa maa ghashshaa

Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.

Aya 55

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىٰ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbika tatamaaraa

To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake yin shakka?

Aya 56

هَٰذَا نَذِيرٌۭ مِّنَ ٱلنُّذُرِ ٱلْأُولَىٰٓ

Haazaa nazeerum minan nuzuril oolaa

wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.

Aya 57

أَزِفَتِ ٱلْءَازِفَةُ

Azifatil laazifah

Makusanciya fa, tã yi kusa.

Aya 58

لَيْسَ لَهَا مِن دُونِ ٱللَّهِ كَاشِفَةٌ

Laisa lahaa min doonil laahi kaashifah

Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.

Aya 59

أَفَمِنْ هَٰذَا ٱلْحَدِيثِ تَعْجَبُونَ

Afamin hazal hadeesi ta'jaboon

Shin, kuma daga wannan lãbãri kuke mãmãki?

Aya 60

وَتَضْحَكُونَ وَلَا تَبْكُونَ

Wa tadhakoona wa laa tabkoon

Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?

Aya 61

وَأَنتُمْ سَٰمِدُونَ

Wa antum saamidoon

Alhãli kunã mãsu wãsã?

Aya 62

فَٱسْجُدُوا۟ لِلَّهِ وَٱعْبُدُوا۟ ۩

Fasjudoo lillaahi wa'budoo

To, ku yi tawãli'u ga Allah, kuma ku bauta (masa).