Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Ƙamar
54

Ƙamar — Wata

القَمَرِ
Makkiyya Aya 55
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

ٱقْتَرَبَتِ ٱلسَّاعَةُ وَٱنشَقَّ ٱلْقَمَرُ

Iqtarabatis Saa'atu wsan shaqqal qamar

Sã'a ta yi kusa, kuma wata ya tsãge.

Aya 2

وَإِن يَرَوْا۟ ءَايَةًۭ يُعْرِضُوا۟ وَيَقُولُوا۟ سِحْرٌۭ مُّسْتَمِرٌّۭ

Wa iny yaraw aayatany yu'ridoo wa yaqooloo sihrum mustamirr

Kuma idan sun ga wata ãyã, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dõgẽwa!"

Aya 3

وَكَذَّبُوا۟ وَٱتَّبَعُوٓا۟ أَهْوَآءَهُمْ ۚ وَكُلُّ أَمْرٍۢ مُّسْتَقِرٌّۭ

Wa kazzaboo wattaba'ooo ahwaaa'ahum; wa kullu amrim mustaqirr

Kuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zũciyarsu, alhãli kuwa kõwane al'amari (wanda suke son su tũre daga Annabi) an tabbatar da shi.

Aya 4

وَلَقَدْ جَآءَهُم مِّنَ ٱلْأَنۢبَآءِ مَا فِيهِ مُزْدَجَرٌ

Wa laqad jaaa'ahum minal ambaaa'i maa feehi muzdajar

Kuma lalle, abin da yake akwai tsãwatarwa a cikinsa na lãbãraiya zo musu.

Aya 5

حِكْمَةٌۢ بَٰلِغَةٌۭ ۖ فَمَا تُغْنِ ٱلنُّذُرُ

Hikmatum baalighatun famaa tughnin nuzur

Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.

Aya 6

فَتَوَلَّ عَنْهُمْ ۘ يَوْمَ يَدْعُ ٱلدَّاعِ إِلَىٰ شَىْءٍۢ نُّكُرٍ

Fatawalla 'anhum; yawma yad'ud daa'i ilaa shai 'in nukur

Sabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.

Aya 7

خُشَّعًا أَبْصَٰرُهُمْ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ كَأَنَّهُمْ جَرَادٌۭ مُّنتَشِرٌۭ

khushsha'an absaaruhum yakrujoona minal ajdaasi ka annahum jaraadum muntashir

¡asƙantattu ga idanunsu zã su fito daga kaburburansu, kamar dai sũ fãri ne waɗandasuka wãtse.

Aya 8

مُّهْطِعِينَ إِلَى ٱلدَّاعِ ۖ يَقُولُ ٱلْكَٰفِرُونَ هَٰذَا يَوْمٌ عَسِرٌۭ

Muhti'eena ilad daa'i yaqoolul kafiroona haazaa yawmun 'asir

Sunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cẽwa, "Wannan yini ne mai wuya!"

Aya 9

۞ كَذَّبَتْ قَبْلَهُمْ قَوْمُ نُوحٍۢ فَكَذَّبُوا۟ عَبْدَنَا وَقَالُوا۟ مَجْنُونٌۭ وَٱزْدُجِرَ

Kazzabat qablahum qawmu Noohin fakazzaboo 'abdanaa wa qaaloo majnoo nunw wazdujir

Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, sai suka ƙaryata BawanMu, kuma suka ce: "Shi mahaukaci ne." Kuma aka tsãwace shi.

Aya 10

فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنِّى مَغْلُوبٌۭ فَٱنتَصِرْ

Fada'aa Rabbahooo annee maghloobun fantasir

Sabõda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle nĩ, an rinjãye ni, sai Ka yi taimako."

Aya 11

فَفَتَحْنَآ أَبْوَٰبَ ٱلسَّمَآءِ بِمَآءٍۢ مُّنْهَمِرٍۢ

Fafatahnaaa abwaabas sa maaa'i bimaa'im munhamir

Sai Muka bũɗe kõfõfin sama da ruwa mai zuba.

Aya 12

وَفَجَّرْنَا ٱلْأَرْضَ عُيُونًۭا فَٱلْتَقَى ٱلْمَآءُ عَلَىٰٓ أَمْرٍۢ قَدْ قُدِرَ

Wa fajjamal arda 'uyoonan faltaqal maaa'u 'alaaa amrin qad qudir

Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙasã ta zama idãnun ruwa, daɗa ruwa ya haɗu a kan wani umurni da aka riga aka ƙaddara shi.

Aya 13

وَحَمَلْنَٰهُ عَلَىٰ ذَاتِ أَلْوَٰحٍۢ وَدُسُرٍۢ

Wa hamalnaahu 'alaa zaati alwaahinw wa dusur

Kuma Muka ɗauke Nũhu a kan (jirgi) na alluna da ƙũsõshi.

Aya 14

تَجْرِى بِأَعْيُنِنَا جَزَآءًۭ لِّمَن كَانَ كُفِرَ

Tajree bi a'yuninaa jazaaa 'al liman kaana kufir

Tanã gudãna, a kan idãnunMu, dõmin sakamako ga wanda aka yi wa kãfircin.

Aya 15

وَلَقَد تَّرَكْنَٰهَآ ءَايَةًۭ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

Wa laqat taraknaahaad aayatan fahal mim muddakir

Kuma lalle, Mun bar ta ta zama ãyã. To, Shin, akwai mai tunãni

Aya 16

فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

Fakaifa kaana 'azaabee wa nuzur

To, yãyã azãbãTa take da gargaɗiNa?

Aya 17

وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

Wa laqad yassamal Quraana liz zikri fahal mimmuddakir

Kuma lalle ne, haƙĩkƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ãni, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

Aya 18

كَذَّبَتْ عَادٌۭ فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

Kazzabat 'Aadun fakaifa kaana 'azaabee wa nuzur

Ãdãwa sun ƙaryata, to, yãya azãbãTa take, da gargaɗiNa?

Aya 19

إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ رِيحًۭا صَرْصَرًۭا فِى يَوْمِ نَحْسٍۢ مُّسْتَمِرٍّۢ

Innaa arsalnaa 'alaihim reehan sarsaran fee Yawmi nahsim mustamirr

Lalle Mũ, Mun aika da iska mai tsananin sauti a kansu, a cikin wani yinin nahĩsa mai dõgẽwa.

Aya 20

تَنزِعُ ٱلنَّاسَ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍۢ مُّنقَعِرٍۢ

Tanzi;un naasa ka anna huma'jaazu nakhlim munqa'ir

Tanã fizgar mutãne kamar dai sũ kututturan dabĩno tumɓukakku ne.

Aya 21

فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

'Fakaifa kaana 'azaabee wa nuzur

To, yãya azãbãTa take da gargaɗiNa?

Aya 22

وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

Wa laqad yassamal Quraana liz zikri fahal mim muddakir

Kuma lalle ne, haƙiƙa Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

Aya 23

كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِٱلنُّذُرِ

Kazzabat Samoodu binnuzur

Samũdãwa sun ƙaryata game da gargaɗin.

Aya 24

فَقَالُوٓا۟ أَبَشَرًۭا مِّنَّا وَٰحِدًۭا نَّتَّبِعُهُۥٓ إِنَّآ إِذًۭا لَّفِى ضَلَٰلٍۢ وَسُعُرٍ

Faqaalooo a-basharam minnaa waahidan nattabi'uhooo innaa izal lafee dalaalinw wa su'ur

Sai suka ce: "Wani mutum daga cikinmu, shi kaɗai, wai mu bĩ shi! Lalle mũ a lõkacin, haƙĩƙa mun shiga wata ɓata da haukã.

Aya 25

أَءُلْقِىَ ٱلذِّكْرُ عَلَيْهِ مِنۢ بَيْنِنَا بَلْ هُوَ كَذَّابٌ أَشِرٌۭ

'A-ulqiyaz zikru 'alaihi mim baininaa bal huwa kazzaabun ashir

"Shin, an jẽfa masa Manzancin ne, a tsakãninmu? Ã'a, shĩ dai gawurtaccen maƙaryaci ne mai girman kai!"

Aya 26

سَيَعْلَمُونَ غَدًۭا مَّنِ ٱلْكَذَّابُ ٱلْأَشِرُ

Sa-ya'lamoona ghadam manil kazzaabul ashir

Zã su sani a gõbe, wãne ne gawurtaccen mai ƙaryar, mai girman kan?

Aya 27

إِنَّا مُرْسِلُوا۟ ٱلنَّاقَةِ فِتْنَةًۭ لَّهُمْ فَٱرْتَقِبْهُمْ وَٱصْطَبِرْ

Innaa mursilun naaqati fitnatal lahum fartaqibhum wastabir

Lalle Mũ, mãsu aikãwa da rãƙumar ne, ta zame musu fitina, sai ka tsare su da kallo, kuma ka yi haƙuri.

Aya 28

وَنَبِّئْهُمْ أَنَّ ٱلْمَآءَ قِسْمَةٌۢ بَيْنَهُمْ ۖ كُلُّ شِرْبٍۢ مُّحْتَضَرٌۭ

Wa nabbi'hum annal maaa'a qismatum bainahum kullu shirbim muhtadar

Kuma ka bã su lãbãri cẽwa ruwa rababbe ne a tsakãninsu (da rãƙumar), kõwane sha, mai shi yanã halartar sa.

Aya 29

فَنَادَوْا۟ صَاحِبَهُمْ فَتَعَاطَىٰ فَعَقَرَ

Fanaadaw saahibahum fata'aataa fa'aqar

Sai suka kira abokinsu, sai ya karɓa, sa'an nan ya sõke ta,

Aya 30

فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

Fakaifa kaana 'azaabee wa nuzur

To, yãya azãbaTa take da gargaɗiNa?

Aya 31

إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ صَيْحَةًۭ وَٰحِدَةًۭ فَكَانُوا۟ كَهَشِيمِ ٱلْمُحْتَظِرِ

Innaaa arsalnaa 'alaihim saihatanw waahidatan fakaano kahasheemil muhtazir

Lalle Mũ, Mun aika tsãwa guda a kansu, sai suka kasance kamar yãyin mai shinge.

Aya 32

وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

Wa laqad yassarnal quraana liz zikri fahal mim muddakir

Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

Aya 33

كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍۭ بِٱلنُّذُرِ

Kazzabat qawmu lootim binnuzur

Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata, game da gargaɗi.

Aya 34

إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ حَاصِبًا إِلَّآ ءَالَ لُوطٍۢ ۖ نَّجَّيْنَٰهُم بِسَحَرٍۢ

Innaa arsalnaa 'alaihim haasiban illaaa aala Loot najjainaahum bisahar

Lalle Mun aika iskar tsakuwa a kansu, fãce mabiyan Lũɗu, Mun tsirar da su a lõkacin asuba.

Aya 35

نِّعْمَةًۭ مِّنْ عِندِنَا ۚ كَذَٰلِكَ نَجْزِى مَن شَكَرَ

Ni'matam min 'indinaa; kazaalika najzee man shakar

Sabõda wata ni'ima ta daga gare Mu. Kamar haka Muke sãka wa wanda ya gõde.

Aya 36

وَلَقَدْ أَنذَرَهُم بَطْشَتَنَا فَتَمَارَوْا۟ بِٱلنُّذُرِ

Wa laqad anzarahum batshatanaa fatamaaraw binnuzur

Kuma lalle, haƙĩƙa, ya yi musu gargaɗin damƙarMu, sai suka yi musu game da gargaɗin.

Aya 37

وَلَقَدْ رَٰوَدُوهُ عَن ضَيْفِهِۦ فَطَمَسْنَآ أَعْيُنَهُمْ فَذُوقُوا۟ عَذَابِى وَنُذُرِ

Wa laqad raawadoohu 'andaifee fatamasnaaa a'yunahum fazooqoo 'azaabee wa nuzur

Kuma lalle haƙĩƙa, su, sun nẽme shi ta wajen bãƙinsa, sai Muka shãfe idãnunsu. "To, ku ɗanɗani azãbaTa da gargaɗĩNa."

Aya 38

وَلَقَدْ صَبَّحَهُم بُكْرَةً عَذَابٌۭ مُّسْتَقِرٌّۭ

Wa laqad sabbahahum bukratan 'azaabum mustaqirr

Kuma lalle, haƙĩƙa, wata azãba matabbaciya tã wãye musu gari da yãƙi, tun da sãfe.

Aya 39

فَذُوقُوا۟ عَذَابِى وَنُذُرِ

Fazooqoo 'azaabee wa nuzur

To, ku ɗanɗani azãbãTa da gargaɗĩNa.

Aya 40

وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

Wa laqad yassarnal Quraana liz zikri fahal mim muddakir

Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur, ani dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

Aya 41

وَلَقَدْ جَآءَ ءَالَ فِرْعَوْنَ ٱلنُّذُرُ

Wa laqad jaaa'a Aala Fir'awnan nuzur

Kuma lalle, haƙĩƙa, gargaɗin ya jẽ wa mabiyan Fir'auna.

Aya 42

كَذَّبُوا۟ بِـَٔايَٰتِنَا كُلِّهَا فَأَخَذْنَٰهُمْ أَخْذَ عَزِيزٍۢ مُّقْتَدِرٍ

Kazzaboo bi Aayaatinaa kullihaa fa akhaznaahum akhza 'azeezim muqtadir

Sun ƙaryata game da ãyõyinMu, dukansu sai Muka kãma su, irin kãmun Mabuwãyi, Mai ĩkon yi.

Aya 43

أَكُفَّارُكُمْ خَيْرٌۭ مِّنْ أُو۟لَٰٓئِكُمْ أَمْ لَكُم بَرَآءَةٌۭ فِى ٱلزُّبُرِ

Akuffaarukum khairum min ulaaa'ikum am lakum baraaa'atun fiz Zubur

Shin, kãfiranku ne mafi alhẽri daga waɗancan, ko kuwa kunã da wata barã'a a cikin littattafai?

Aya 44

أَمْ يَقُولُونَ نَحْنُ جَمِيعٌۭ مُّنتَصِرٌۭ

Am yaqooloona nahnu jamee'um muntasir

Kõ zã su ce: "Mũ duka mãsu haɗa ƙarfi ne dõmin cin nasara?"

Aya 45

سَيُهْزَمُ ٱلْجَمْعُ وَيُوَلُّونَ ٱلدُّبُرَ

Sa yuhzamul jam'u wa yuwalloonad dubur

Zã a karya tãron, kuma su jũya bãya dõmin gudu.

Aya 46

بَلِ ٱلسَّاعَةُ مَوْعِدُهُمْ وَٱلسَّاعَةُ أَدْهَىٰ وَأَمَرُّ

Balis Saa'atu maw'iduhum was Saa'atu adhaa wa amarr

Ã'a, Sã'a ita cẽ lõkacin wa'adinsu, kuma Sã'ar tã fi tsananin masĩfa, kuma ta fiɗãci.

Aya 47

إِنَّ ٱلْمُجْرِمِينَ فِى ضَلَٰلٍۢ وَسُعُرٍۢ

Innal mujrimeena fee dalaalinw wa su'ur

Lalle ne, mãsu laifi sunã a cikin ɓata da hauka.

Aya 48

يَوْمَ يُسْحَبُونَ فِى ٱلنَّارِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمْ ذُوقُوا۟ مَسَّ سَقَرَ

Yawma yushaboona fin Naari'alaa wujoohimim zooqoo massa saqar

Rãnar da zã a jã su a cikin wuta a kan fuskõkinsu. "Ku ɗanɗani shãfar wutar Saƙar."

Aya 49

إِنَّا كُلَّ شَىْءٍ خَلَقْنَٰهُ بِقَدَرٍۢ

Innaa kulla shai'in khalaqnaahu biqadar

Lalle Mũ, kõwane irin abu Mun halitta shi a kan tsãri.

Aya 50

وَمَآ أَمْرُنَآ إِلَّا وَٰحِدَةٌۭ كَلَمْحٍۭ بِٱلْبَصَرِ

Wa maaa amrunaaa illaa waahidatun kalamhim bilbasar

Kuma umurninMu bai zamo ba fãce da kalma ɗaya, kamar walƙãwar ido.

Aya 51

وَلَقَدْ أَهْلَكْنَآ أَشْيَاعَكُمْ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ

Wa laqad ahlaknaaa ashyaa'akum fahal mim muddakir

Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun halaka irin gayyarku. To, shin, akwai mai tunãni?

Aya 52

وَكُلُّ شَىْءٍۢ فَعَلُوهُ فِى ٱلزُّبُرِ

Wa kullu shai'in fa'aloohu fiz Zubur

Kuma kõwane abu, da suka aikata shi, yanã a cikin littattafai.

Aya 53

وَكُلُّ صَغِيرٍۢ وَكَبِيرٍۢ مُّسْتَطَرٌ

Wa kullu sagheerinw wa kabeerim mustatar

Kuma dukkan ƙarami da babba, rubutacce ne.

Aya 54

إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّٰتٍۢ وَنَهَرٍۢ

Innal muttaqeena fee jannaatinw wa nahar

Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna da kõguna.

Aya 55

فِى مَقْعَدِ صِدْقٍ عِندَ مَلِيكٍۢ مُّقْتَدِرٍۭ

Fee maq'adi sidqin 'inda Maleekim Muqtadir

A cikin mazaunin gaskiya, wurin Mai ikon yi, Mai iya zartaswa.