Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Rahman
55

Rahman — Mai Rahama

الرَّحۡمَٰن
Madaniyya Aya 78
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

ٱلرَّحْمَٰنُ

Ar Rahmaan

(Allah) Mai rahama.

Aya 2

عَلَّمَ ٱلْقُرْءَانَ

'Allamal Quran

Yã sanar da Alƙur'ani.

Aya 3

خَلَقَ ٱلْإِنسَٰنَ

Khalaqal insaan

Yã halitta mutum.

Aya 4

عَلَّمَهُ ٱلْبَيَانَ

'Allamalhul bayaan

Yã sanar da shi bayãni (magana).

Aya 5

ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ بِحُسْبَانٍۢ

Ashshamsu walqamaru bihusbaan

Rãnã da watã a kan lissãfi suke.

Aya 6

وَٱلنَّجْمُ وَٱلشَّجَرُ يَسْجُدَانِ

Wannajmu washshajaru yasjudan

Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.

Aya 7

وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلْمِيزَانَ

Wassamaaa'a rafa'ahaa wa wada'al Meezan

Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.

Aya 8

أَلَّا تَطْغَوْا۟ فِى ٱلْمِيزَانِ

Allaa tatghaw fil meezaan

Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.

Aya 9

وَأَقِيمُوا۟ ٱلْوَزْنَ بِٱلْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا۟ ٱلْمِيزَانَ

Wa aqeemul wazna bilqisti wa laa tukhsirul meezaan

Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.

Aya 10

وَٱلْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ

Wal arda wada'ahaa lilanaame

Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.

Aya 11

فِيهَا فَٰكِهَةٌۭ وَٱلنَّخْلُ ذَاتُ ٱلْأَكْمَامِ

Feehaa faakihatunw wan nakhlu zaatul akmaam

A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.

Aya 12

وَٱلْحَبُّ ذُو ٱلْعَصْفِ وَٱلرَّيْحَانُ

Walhabbu zul 'asfi war Raihaanu

Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.

Aya 13

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?

Aya 14

خَلَقَ ٱلْإِنسَٰنَ مِن صَلْصَٰلٍۢ كَٱلْفَخَّارِ

Khalaqal insaana min salsaalin kalfakhkhaari

Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.

Aya 15

وَخَلَقَ ٱلْجَآنَّ مِن مَّارِجٍۢ مِّن نَّارٍۢ

Wa khalaqal jaaan mim maarijim min naar

Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.

Aya 16

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 17

رَبُّ ٱلْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ ٱلْمَغْرِبَيْنِ

Rabbul mashriqayni wa Rabbul maghribayni

Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.

Aya 18

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 19

مَرَجَ ٱلْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ

Marajal bahrayni yalta qiyaani

Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.

Aya 20

بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌۭ لَّا يَبْغِيَانِ

Bainahumaa barzakhul laa yabghiyaan

A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.

Aya 21

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 22

يَخْرُجُ مِنْهُمَا ٱللُّؤْلُؤُ وَٱلْمَرْجَانُ

Yakhruju minhumal lu 'lu u wal marjaanu

Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.

Aya 23

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 24

وَلَهُ ٱلْجَوَارِ ٱلْمُنشَـَٔاتُ فِى ٱلْبَحْرِ كَٱلْأَعْلَٰمِ

Wa lahul jawaaril mun sha'aatu fil bahri kal a'laam

Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.

Aya 25

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 26

كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍۢ

Kullu man 'alaihaa faan

Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.

Aya 27

وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو ٱلْجَلَٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ

Wa yabqaa wajhu rabbika zul jalaali wal ikraam

Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.

Aya 28

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 29

يَسْـَٔلُهُۥ مَن فِى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِى شَأْنٍۢ

Yas'aluhoo man fissamaawaati walard; kulla ywmin huwa fee shaan

wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.

Aya 30

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 31

سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ

Sanafrughu lakum ayyuhas saqalaan

Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!

Aya 32

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 33

يَٰمَعْشَرَ ٱلْجِنِّ وَٱلْإِنسِ إِنِ ٱسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا۟ مِنْ أَقْطَارِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ فَٱنفُذُوا۟ ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَٰنٍۢ

Yaa ma'sharal jinni wal insi inis tata'tum an tanfuzoo min aqtaaris samaawaati wal ardi fanfuzoo; laa tanfuzoona illaa bisultaan

Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.

Aya 34

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 35

يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌۭ مِّن نَّارٍۢ وَنُحَاسٌۭ فَلَا تَنتَصِرَانِ

Yursalu 'alaikumaa shuwaazum min naarifiw-wa nuhaasun falaa tantasiraan

Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?

Aya 36

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 37

فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ وَرْدَةًۭ كَٱلدِّهَانِ

Fa-izan shaqqatis samaaa'u fakaanat wardatan kaddihaan

Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.

Aya 38

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 39

فَيَوْمَئِذٍۢ لَّا يُسْـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٌۭ وَلَا جَآنٌّۭ

Fa-yawma'izil laa yus'alu 'an zambiheee insunw wa laa jaann

To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.

Aya 40

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 41

يُعْرَفُ ٱلْمُجْرِمُونَ بِسِيمَٰهُمْ فَيُؤْخَذُ بِٱلنَّوَٰصِى وَٱلْأَقْدَامِ

Yu'raful mujrimoona biseemaahum fa'yu'khazu binna waasi wal aqdaam

zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.

Aya 42

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 43

هَٰذِهِۦ جَهَنَّمُ ٱلَّتِى يُكَذِّبُ بِهَا ٱلْمُجْرِمُونَ

Haazihee jahannamul latee yukazzibu bihal mujrimoon

Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.

Aya 44

يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ ءَانٍۢ

Yatoofoona bainahaa wa baina hameemim aan

Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.

Aya 45

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 46

وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ

Wa liman khaafa maqaama rabbihee jannataan

Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.

Aya 47

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 48

ذَوَاتَآ أَفْنَانٍۢ

Zawaataaa afnaan

Mãsu rassan itãce.

Aya 49

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 50

فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ

Feehimaa 'aynaani tajriyaan

A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.

Aya 51

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 52

فِيهِمَا مِن كُلِّ فَٰكِهَةٍۢ زَوْجَانِ

Feehimaa min kulli faakihatin zawjaan

A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.

Aya 53

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 54

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ فُرُشٍۭ بَطَآئِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍۢ ۚ وَجَنَى ٱلْجَنَّتَيْنِ دَانٍۢ

Muttaki'eena 'alaa furushim bataaa'inuhaa min istabraq; wajanal jannataini daan

Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.

Aya 55

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 56

فِيهِنَّ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌۭ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّۭ

Feehinna qaasiratut tarfi lam yatmishunna insun qablahum wa laa jaaann

A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.

Aya 57

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 58

كَأَنَّهُنَّ ٱلْيَاقُوتُ وَٱلْمَرْجَانُ

ka annahunnal yaaqootu wal marjaan

Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.

Aya 59

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 60

هَلْ جَزَآءُ ٱلْإِحْسَٰنِ إِلَّا ٱلْإِحْسَٰنُ

Hal jazaaa'ul ihsaani illal ihsaan

Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.

Aya 61

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 62

وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ

Wa min doonihimaa jannataan

Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.

Aya 63

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 64

مُدْهَآمَّتَانِ

Mudhaaammataan

Mãsu duhun inuwa.

Aya 65

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 66

فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ

Feehimaa 'aynaani nad daakhataan

A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.

Aya 67

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 68

فِيهِمَا فَٰكِهَةٌۭ وَنَخْلٌۭ وَرُمَّانٌۭ

Feehimaa faakihatunw wa nakhlunw wa rummaan

A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.

Aya 69

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 70

فِيهِنَّ خَيْرَٰتٌ حِسَانٌۭ

Feehinna khairaatun hisaan

A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.

Aya 71

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 72

حُورٌۭ مَّقْصُورَٰتٌۭ فِى ٱلْخِيَامِ

Hoorum maqsooraatun fil khiyaam

Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.

Aya 73

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 74

لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌۭ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّۭ

Lam yatmis hunna insun qablahum wa laa jaaann

Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.

Aya 75

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 76

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍۢ وَعَبْقَرِىٍّ حِسَانٍۢ

Muttaki'eena 'alaa rafratin khudrinw wa 'abqariyyin hisaan

Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.

Aya 77

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Fabi ayyi aalaaa'i Rabbikumaa tukazzibaan.

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Aya 78

تَبَٰرَكَ ٱسْمُ رَبِّكَ ذِى ٱلْجَلَٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ

Tabaarakasmu Rabbika Zil-Jalaali wal-Ikraam

Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.