Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Waƙi'a
56

Waƙi'a — Abin Aukuwa

الوَاقِعَةِ
Makkiyya Aya 96
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

إِذَا وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ

Izaa waqa'atil waaqi'ah

Idan mai aukuwa ta auku.

Aya 2

لَيْسَ لِوَقْعَتِهَا كَاذِبَةٌ

Laisa liwaq'atihaa kaazibah

Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.

Aya 3

خَافِضَةٌۭ رَّافِعَةٌ

Khafidatur raafi'ah

(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.

Aya 4

إِذَا رُجَّتِ ٱلْأَرْضُ رَجًّۭا

Izaa rujjatil ardu rajjaa

Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.

Aya 5

وَبُسَّتِ ٱلْجِبَالُ بَسًّۭا

Wa bussatil jibaalu bassaa

Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.

Aya 6

فَكَانَتْ هَبَآءًۭ مُّنۢبَثًّۭا

Fakaanat habaaa'am mumbassaa

Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.

Aya 7

وَكُنتُمْ أَزْوَٰجًۭا ثَلَٰثَةًۭ

Wa kuntum azwaajan salaasah

Kuma kun kasance nau'i uku.

Aya 8

فَأَصْحَٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ

Fa as haabul maimanati maaa as haabul maimanah

Watau mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?

Aya 9

وَأَصْحَٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ

Wa as haabul mash'amati maaa as haabul mash'amah

Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?

Aya 10

وَٱلسَّٰبِقُونَ ٱلسَّٰبِقُونَ

Wassaabiqoonas saabiqoon

Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,

Aya 11

أُو۟لَٰٓئِكَ ٱلْمُقَرَّبُونَ

Ulaaa'ikal muqarraboon

Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.

Aya 12

فِى جَنَّٰتِ ٱلنَّعِيمِ

Fee Jannaatin Na'eem

A ckin Aljannar ni'ima.

Aya 13

ثُلَّةٌۭ مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ

Sullatum minal awwaleen

Jama'a ne daga mutãnen farko.

Aya 14

وَقَلِيلٌۭ مِّنَ ٱلْءَاخِرِينَ

Wa qaleelum minal aa khireen

Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.

Aya 15

عَلَىٰ سُرُرٍۢ مَّوْضُونَةٍۢ

'Alaa sururim mawdoonah

(Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.

Aya 16

مُّتَّكِـِٔينَ عَلَيْهَا مُتَقَٰبِلِينَ

Muttaki'eena 'alaihaa mutaqabileen

Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.

Aya 17

يَطُوفُ عَلَيْهِمْ وِلْدَٰنٌۭ مُّخَلَّدُونَ

Yatoofu 'alaihim wildaa num mukkhalladoon

Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.

Aya 18

بِأَكْوَابٍۢ وَأَبَارِيقَ وَكَأْسٍۢ مِّن مَّعِينٍۢ

Bi akwaabinw wa abaareeq, wa kaasim mim ma'een

Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.

Aya 19

لَّا يُصَدَّعُونَ عَنْهَا وَلَا يُنزِفُونَ

Laa yusadda'oona 'anhaa wa laa yunzifoon

Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.

Aya 20

وَفَٰكِهَةٍۢ مِّمَّا يَتَخَيَّرُونَ

Wa faakihatim mimmaa yatakhaiyaroon

Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.

Aya 21

وَلَحْمِ طَيْرٍۢ مِّمَّا يَشْتَهُونَ

Wa lahmi tairim mimmaa yashtahoon

Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.

Aya 22

وَحُورٌ عِينٌۭ

Wa hoorun'een

Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.

Aya 23

كَأَمْثَٰلِ ٱللُّؤْلُؤِ ٱلْمَكْنُونِ

Ka amsaalil lu'lu'il maknoon

Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.

Aya 24

جَزَآءًۢ بِمَا كَانُوا۟ يَعْمَلُونَ

Jazaaa'am bimaa kaanoo ya'maloon

A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.

Aya 25

لَا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًۭا وَلَا تَأْثِيمًا

Laa yasma'oona feehaa laghwanw wa laa taaseemaa

Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.

Aya 26

إِلَّا قِيلًۭا سَلَٰمًۭا سَلَٰمًۭا

Illaa qeelan salaaman salaamaa

Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.

Aya 27

وَأَصْحَٰبُ ٱلْيَمِينِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلْيَمِينِ

Wa as haabul yameeni maaa as haabul Yameen

Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?

Aya 28

فِى سِدْرٍۢ مَّخْضُودٍۢ

Fee sidrim makhdood

(Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.

Aya 29

وَطَلْحٍۢ مَّنضُودٍۢ

Wa talhim mandood

Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.

Aya 30

وَظِلٍّۢ مَّمْدُودٍۢ

Wa zillim mamdood

Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.

Aya 31

وَمَآءٍۢ مَّسْكُوبٍۢ

Wa maaa'im maskoob

Da wani ruwa mai gudãna.

Aya 32

وَفَٰكِهَةٍۢ كَثِيرَةٍۢ

Wa faakihatin kaseerah

Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.

Aya 33

لَّا مَقْطُوعَةٍۢ وَلَا مَمْنُوعَةٍۢ

Laa maqtoo'atinw wa laa mamnoo'ah

Bã su yankẽwa kuma bã a hana su.

Aya 34

وَفُرُشٍۢ مَّرْفُوعَةٍ

Wa furushim marfoo'ah

Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.

Aya 35

إِنَّآ أَنشَأْنَٰهُنَّ إِنشَآءًۭ

Innaaa anshaanaahunna inshaaa'aa

Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.

Aya 36

فَجَعَلْنَٰهُنَّ أَبْكَارًا

Faja'alnaahunna abkaaraa

Sa'an nan Muka sanya su budurwai.

Aya 37

عُرُبًا أَتْرَابًۭا

'Uruban atraabaa

Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.

Aya 38

لِّأَصْحَٰبِ ٱلْيَمِينِ

Li as haabil yameen

Ga mazõwa dãma.

Aya 39

ثُلَّةٌۭ مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ

Sullatum minal awwa leen

Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.

Aya 40

وَثُلَّةٌۭ مِّنَ ٱلْءَاخِرِينَ

Wa sullatum minal aakhireen

Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.

Aya 41

وَأَصْحَٰبُ ٱلشِّمَالِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلشِّمَالِ

Wa as haabush shimaali maaa as haabush shimaal

Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?

Aya 42

فِى سَمُومٍۢ وَحَمِيمٍۢ

Fee samoominw wa hameem

Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.

Aya 43

وَظِلٍّۢ مِّن يَحْمُومٍۢ

Wa zillim miny yahmoom

Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.

Aya 44

لَّا بَارِدٍۢ وَلَا كَرِيمٍ

Laa baaridinw wa laa kareem

Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.

Aya 45

إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَبْلَ ذَٰلِكَ مُتْرَفِينَ

Innaahum kaanoo qabla zaalika mutrafeen

Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.

Aya 46

وَكَانُوا۟ يُصِرُّونَ عَلَى ٱلْحِنثِ ٱلْعَظِيمِ

Wa kaanoo yusirroona 'alal hinsil 'azeem

Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.

Aya 47

وَكَانُوا۟ يَقُولُونَ أَئِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًۭا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ

Wa kaanoo yaqooloona a'izaa mitnaa wa kunnaa turaabanw wa izaaman'ainnaa lamab'oosoon

Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"

Aya 48

أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ

Awa aabaaa'unal awwaloon

"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"

Aya 49

قُلْ إِنَّ ٱلْأَوَّلِينَ وَٱلْءَاخِرِينَ

Qul innal awwaleena wal aakhireen

Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."

Aya 50

لَمَجْمُوعُونَ إِلَىٰ مِيقَٰتِ يَوْمٍۢ مَّعْلُومٍۢ

Lamajmoo'oona ilaa meeqaati yawmim ma'loon

"Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."

Aya 51

ثُمَّ إِنَّكُمْ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلْمُكَذِّبُونَ

summa innakum ayyuhad daaalloonal mukazziboon

"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"

Aya 52

لَءَاكِلُونَ مِن شَجَرٍۢ مِّن زَقُّومٍۢ

La aakiloona min shaja rim min zaqqoom

"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."

Aya 53

فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ

Famaali'oona minhal butoon

"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."

Aya 54

فَشَٰرِبُونَ عَلَيْهِ مِنَ ٱلْحَمِيمِ

Fashaariboona 'alaihi minal hameem

"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."

Aya 55

فَشَٰرِبُونَ شُرْبَ ٱلْهِيمِ

Fashaariboona shurbal heem

"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."

Aya 56

هَٰذَا نُزُلُهُمْ يَوْمَ ٱلدِّينِ

Haazaa nuzuluhum yawmad deen

Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.

Aya 57

نَحْنُ خَلَقْنَٰكُمْ فَلَوْلَا تُصَدِّقُونَ

Nahnu khalaqnaakum falaw laa tusaddiqoon

Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?

Aya 58

أَفَرَءَيْتُم مَّا تُمْنُونَ

Afara'aytum maa tumnoon

Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?

Aya 59

ءَأَنتُمْ تَخْلُقُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلْخَٰلِقُونَ

'A-antum takhluqoo nahooo am nahnul khaaliqoon

Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?

Aya 60

نَحْنُ قَدَّرْنَا بَيْنَكُمُ ٱلْمَوْتَ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ

Nahnu qaddarnaa baina kumul mawta wa maa nahnu bimasbooqeen

Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba,

Aya 61

عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ أَمْثَٰلَكُمْ وَنُنشِئَكُمْ فِى مَا لَا تَعْلَمُونَ

'Alaaa an nubaddila amsaalakum wa nunshi'akum fee maa laa ta'lamoon

A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.

Aya 62

وَلَقَدْ عَلِمْتُمُ ٱلنَّشْأَةَ ٱلْأُولَىٰ فَلَوْلَا تَذَكَّرُونَ

Wa laqad 'alimtumun nash atal oolaa falaw laa tazakkaroon

Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?

Aya 63

أَفَرَءَيْتُم مَّا تَحْرُثُونَ

Afara'aytum maa tahrusoon

Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?

Aya 64

ءَأَنتُمْ تَزْرَعُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلزَّٰرِعُونَ

'A-antum tazra'oonahooo am nahnuz zaari'ooon

Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?

Aya 65

لَوْ نَشَآءُ لَجَعَلْنَٰهُ حُطَٰمًۭا فَظَلْتُمْ تَفَكَّهُونَ

Law nashaaa'u laja'al naahu hutaaman fazaltum tafakkahoon

Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.

Aya 66

إِنَّا لَمُغْرَمُونَ

Innaa lamughramoon

(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"

Aya 67

بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ

Bal nahnu mahroomoon

"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"

Aya 68

أَفَرَءَيْتُمُ ٱلْمَآءَ ٱلَّذِى تَشْرَبُونَ

Afara'aytumul maaa'allazee tashraboon

Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?

Aya 69

ءَأَنتُمْ أَنزَلْتُمُوهُ مِنَ ٱلْمُزْنِ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنزِلُونَ

'A-antum anzaltumoohu minal muzni am nahnul munziloon

Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?

Aya 70

لَوْ نَشَآءُ جَعَلْنَٰهُ أُجَاجًۭا فَلَوْلَا تَشْكُرُونَ

Law nashaaa'u ja'alnaahu ujaajan falaw laa tashkuroon

Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?

Aya 71

أَفَرَءَيْتُمُ ٱلنَّارَ ٱلَّتِى تُورُونَ

Afara'aytumun naaral latee tooroon

Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?

Aya 72

ءَأَنتُمْ أَنشَأْتُمْ شَجَرَتَهَآ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنشِـُٔونَ

'A-antum anshaatum shajaratahaaa am nahnul munshi'oon

Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?

Aya 73

نَحْنُ جَعَلْنَٰهَا تَذْكِرَةًۭ وَمَتَٰعًۭا لِّلْمُقْوِينَ

Nahnu ja'alnaahaa tazkira tanw wa mataa'al lilmuqween

Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.

Aya 74

فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ

Fasabbih bismi Rabbikal 'azeem

Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.

Aya 75

۞ فَلَآ أُقْسِمُ بِمَوَٰقِعِ ٱلنُّجُومِ

Falaa uqsimu bimaawaa qi'innujoom

To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.

Aya 76

وَإِنَّهُۥ لَقَسَمٌۭ لَّوْ تَعْلَمُونَ عَظِيمٌ

Wa innahoo laqasamul lawta'lamoona'azeem

Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.

Aya 77

إِنَّهُۥ لَقُرْءَانٌۭ كَرِيمٌۭ

Innahoo la quraanun kareem

Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.

Aya 78

فِى كِتَٰبٍۢ مَّكْنُونٍۢ

Fee kitaabim maknoon

A cikin wani littafi tsararre.

Aya 79

لَّا يَمَسُّهُۥٓ إِلَّا ٱلْمُطَهَّرُونَ

Laa yamassuhooo illal mutahharoon

Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.

Aya 80

تَنزِيلٌۭ مِّن رَّبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Tanzeelum mir Rabbil'aalameen

Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.

Aya 81

أَفَبِهَٰذَا ٱلْحَدِيثِ أَنتُم مُّدْهِنُونَ

Afabihaazal hadeesi antum mudhinoon

Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?

Aya 82

وَتَجْعَلُونَ رِزْقَكُمْ أَنَّكُمْ تُكَذِّبُونَ

Wa taj'aloona rizqakum annakum tukazziboon

Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?

Aya 83

فَلَوْلَآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلْحُلْقُومَ

Falaw laaa izaa balaghatil hulqoom

To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).

Aya 84

وَأَنتُمْ حِينَئِذٍۢ تَنظُرُونَ

Wa antum heena'izin tanzuroon

Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.

Aya 85

وَنَحْنُ أَقْرَبُ إِلَيْهِ مِنكُمْ وَلَٰكِن لَّا تُبْصِرُونَ

Wa nahnu aqrabu ilaihi minkum wa laakil laa tubsiroon

Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.

Aya 86

فَلَوْلَآ إِن كُنتُمْ غَيْرَ مَدِينِينَ

Falaw laaa in kuntum ghira madeeneen

To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?

Aya 87

تَرْجِعُونَهَآ إِن كُنتُمْ صَٰدِقِينَ

Tarji'oonahaaa in kuntum saadiqeen

Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.

Aya 88

فَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُقَرَّبِينَ

Fa ammaaa in kaana minal muqarrabeen

To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,

Aya 89

فَرَوْحٌۭ وَرَيْحَانٌۭ وَجَنَّتُ نَعِيمٍۢ

Farawhunw wa raihaa nunw wa jannatu na'eem

Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.

Aya 90

وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنْ أَصْحَٰبِ ٱلْيَمِينِ

Wa ammaaa in kaana min as haabil yameen

Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,

Aya 91

فَسَلَٰمٌۭ لَّكَ مِنْ أَصْحَٰبِ ٱلْيَمِينِ

Fasalaamul laka min as haabil yameen

Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.

Aya 92

وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُكَذِّبِينَ ٱلضَّآلِّينَ

Wa ammaaa in kaana minal mukazzibeenad daaalleen

Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,

Aya 93

فَنُزُلٌۭ مِّنْ حَمِيمٍۢ

Fanuzulum min hameem

Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.

Aya 94

وَتَصْلِيَةُ جَحِيمٍ

Wa tasliyatu jaheem

Da ƙõnuwa da Jahĩm,

Aya 95

إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ حَقُّ ٱلْيَقِينِ

Inna haaza lahuwa haqqul yaqeen

Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.

Aya 96

فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ

Fasabbih bismi rabbikal 'azeem

Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.