Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / A'ala
87

A'ala — Maɗaukaki

الأَعۡلَىٰ
Makkiyya Aya 19
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

سَبِّحِ ٱسْمَ رَبِّكَ ٱلْأَعْلَى

Sabbihisma Rabbikal A'laa

Ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mafi ɗaukaka.

Aya 2

ٱلَّذِى خَلَقَ فَسَوَّىٰ

Allazee khalaqa fasawwaa

Wanda Yã yi halitta sa'an nan Ya daidaita abin halittar.

Aya 3

وَٱلَّذِى قَدَّرَ فَهَدَىٰ

Wallazee qaddara fahadaa

Kuma Wanda Ya ƙaddara (abin da Ya so) sannan Ya shiryar, (da mutum ga hanyar alhẽri da ta sharri).

Aya 4

وَٱلَّذِىٓ أَخْرَجَ ٱلْمَرْعَىٰ

Wallazeee akhrajal mar'aa

Kuma Wanda Ya fitar da makiyãyã.

Aya 5

فَجَعَلَهُۥ غُثَآءً أَحْوَىٰ

Faja'alahoo ghusaaa'an ahwaa

Sa'an nan Ya mayar da ita ƙeƙasassa, baƙa.

Aya 6

سَنُقْرِئُكَ فَلَا تَنسَىٰٓ

Sanuqri'uka falaa tansaaa

Za mu karantar da kai (Alƙur'ãni) sabõda haka bã zã ka mantã (shi) ba.

Aya 7

إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُ ۚ إِنَّهُۥ يَعْلَمُ ٱلْجَهْرَ وَمَا يَخْفَىٰ

Illaa maa shaaa'al laah; innahoo ya'lamul jahra wa maa yakhfaa

Fãce abin da Allah Ya so, lalle ne Shi (Allah) Ya san bayyane da abin da yake bõye.

Aya 8

وَنُيَسِّرُكَ لِلْيُسْرَىٰ

Wa nu-yassiruka lilyusraa

Kuma za Mu sauƙaƙe maka (al'amari) zuwa ga (Shari'a) mai sauƙi.

Aya 9

فَذَكِّرْ إِن نَّفَعَتِ ٱلذِّكْرَىٰ

Fazakkir in nafa'atizzikraa

Sabõda baka, ka tunãtar, idan tunatarwa zã ta yi amfãni.

Aya 10

سَيَذَّكَّرُ مَن يَخْشَىٰ

Sa yazzakkaru maiyakhshaa

Wanda yake tsõron (Allah) Zai tuna.

Aya 11

وَيَتَجَنَّبُهَا ٱلْأَشْقَى

Wa yatajannabuhal ashqaa

Kuma shaƙiyyi, zai nisanceta,

Aya 12

ٱلَّذِى يَصْلَى ٱلنَّارَ ٱلْكُبْرَىٰ

Allazee yaslan Naaral kubraa

Wanda zai shiga wutar da tã fi girma.

Aya 13

ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحْيَىٰ

Summa laa yamootu feehaa wa laa yahyaa

Sa'an nan bã zai mutu ba a cikinta, kuma bã zai rãyu ba.

Aya 14

قَدْ أَفْلَحَ مَن تَزَكَّىٰ

Qad aflaha man tazakkaa

Lalle ne wanda ya tsarkaka (da ĩmãni) yã sãmu babban rabo.

Aya 15

وَذَكَرَ ٱسْمَ رَبِّهِۦ فَصَلَّىٰ

Wa zakaras ma Rabbihee fasallaa

Kuma ya ambaci sũnan Ubangijinsa, sa'an nan yã yi salla.

Aya 16

بَلْ تُؤْثِرُونَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا

Bal tu'siroonal hayaatad dunyaa

Ba haka ba! Kunã zãɓin rãyuwa ta kusa dũniya.

Aya 17

وَٱلْءَاخِرَةُ خَيْرٌۭ وَأَبْقَىٰٓ

Wal Aakhiratu khairunw wa abqaa

Alhãli Lãhira ita ce mafi alheri kuma mafi wanzuwa.

Aya 18

إِنَّ هَٰذَا لَفِى ٱلصُّحُفِ ٱلْأُولَىٰ

Inna haazaa lafis suhu fil oolaa

Lalle ne, wannan yanã a cikin littafan farko.

Aya 19

صُحُفِ إِبْرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ

Suhufi Ibraaheema wa Moosaa

Littaffan Ibrãhĩm da Mũsã.