Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Gashiya
88

Gashiya — Mai Rufewa

الغَاشِيَةِ
Makkiyya Aya 26
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلْغَٰشِيَةِ

Hal ataaka hadeesul ghaashiyah

Lalle ne labãrin (¡iyãma) mai rufe mutãne da tsoronta yã zo maka?

Aya 2

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍ خَٰشِعَةٌ

Wujoohuny yawma 'izin khaashi'ah

Wasu huskõki a rãnar nan ƙasƙantattu ne.

Aya 3

عَامِلَةٌۭ نَّاصِبَةٌۭ

'Aamilatun naasibah

Mãsu aikin wahala ne, mãsu gajiya.

Aya 4

تَصْلَىٰ نَارًا حَامِيَةًۭ

Taslaa naaran haamiyah

Zã su shiga wata wuta mai zãfi.

Aya 5

تُسْقَىٰ مِنْ عَيْنٍ ءَانِيَةٍۢ

Tusqaa min 'aynin aaniyah

Ana shãyar da su daga wani marmaro mai zãfin ruwa.

Aya 6

لَّيْسَ لَهُمْ طَعَامٌ إِلَّا مِن ضَرِيعٍۢ

Laisa lahum ta'aamun illaa min daree'

Ba su da wani abinci fãce dai daga danyi.

Aya 7

لَّا يُسْمِنُ وَلَا يُغْنِى مِن جُوعٍۢ

Laa yusminu wa laa yughnee min joo'

Bã ya sanya ƙiba, kuma bã zai wadãtar daga yunwa ba.

Aya 8

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ نَّاعِمَةٌۭ

Wujoohuny yawma 'izin naa'imah

Wasu huskõki a rãnar nan mãsu ni'ima ne.

Aya 9

لِّسَعْيِهَا رَاضِيَةٌۭ

Lisa'yihaa raadiyah

Game da aikinsu, masu yarda ne.

Aya 10

فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍۢ

Fee jannatin 'aaliyah

(Suna) a cikin Aljanna maɗaukakiya.

Aya 11

لَّا تَسْمَعُ فِيهَا لَٰغِيَةًۭ

Laa tasma'u feehaa laaghiyah

Bã zã su ji yãsassar magana ba, a cikinta.

Aya 12

فِيهَا عَيْنٌۭ جَارِيَةٌۭ

Feehaa 'aynun jaariyah

A cikinta akwai marmaro mai gudãna.

Aya 13

فِيهَا سُرُرٌۭ مَّرْفُوعَةٌۭ

Feehaa sururum marfoo'ah

A cikinta akwai gadãje maɗaukaka.

Aya 14

وَأَكْوَابٌۭ مَّوْضُوعَةٌۭ

Wa akwaabum mawdoo 'ah

Da kõfuna ar'aje.

Aya 15

وَنَمَارِقُ مَصْفُوفَةٌۭ

Wa namaariqu masfoofah

Da filõli jẽre,

Aya 16

وَزَرَابِىُّ مَبْثُوثَةٌ

Wa zaraabiyyu mabsoosah

Da katifu shimfiɗe.

Aya 17

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلْإِبِلِ كَيْفَ خُلِقَتْ

Afalaa yanzuroona ilalibili kaifa khuliqat

Ashe to bã zã su dũbãwa ba ga rãƙumã yadda aka halitta su?

Aya 18

وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيْفَ رُفِعَتْ

Wa ilas samaaa'i kaifa rufi'at

Da zuwa ga sama yadda aka ɗaukaka ta?

Aya 19

وَإِلَى ٱلْجِبَالِ كَيْفَ نُصِبَتْ

Wa ilal jibaali kaifa nusibat

Da zuwa ga duwãtsu yadda aka kafa su?

Aya 20

وَإِلَى ٱلْأَرْضِ كَيْفَ سُطِحَتْ

Wa ilal ardi kaifa sutihat

Da zuwa ga ƙasa yadda aka shimfiɗã ta?

Aya 21

فَذَكِّرْ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٌۭ

Fazakkir innama anta Muzakkir

sabõda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai.

Aya 22

لَّسْتَ عَلَيْهِم بِمُصَيْطِرٍ

Lasta 'alaihim bimusaitir

Ba ka zama mai ĩkon tanƙwasãwa a kansu ba.

Aya 23

إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ

Illaa man tawallaa wa kafar

Fãce dai duk wanda ya jũya bãya, kuma ya kãfirta.

Aya 24

فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَكْبَرَ

Fa yu'azzibuhul laahul 'azaabal akbar

To, Allah zai yi masa azãba, azãbar nan da take mafi girma.

Aya 25

إِنَّ إِلَيْنَآ إِيَابَهُمْ

Innaa ilainaaa iyaabahum

Lalle ne, zuwa gare Mu kõmõwarsu take.

Aya 26

ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا حِسَابَهُم

Summa inna 'alainaa hisaabahum

Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisãbi.