Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Fajr
89

Fajr — Alfijir

الفَجۡرِ
Makkiyya Aya 30
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَٱلْفَجْرِ

Wal-Fajr

Inã rantsuwa da alfijiri.

Aya 2

وَلَيَالٍ عَشْرٍۢ

Wa layaalin 'ashr

Da darũruwa gõma.

Aya 3

وَٱلشَّفْعِ وَٱلْوَتْرِ

Wash shaf'i wal watr

Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.

Aya 4

وَٱلَّيْلِ إِذَا يَسْرِ

Wallaili izaa yasr

Da dare idan yana shũɗewa.

Aya 5

هَلْ فِى ذَٰلِكَ قَسَمٌۭ لِّذِى حِجْرٍ

Hal fee zaalika qasamul lizee hijr

Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?

Aya 6

أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ

Alam tara kaifa fa'ala rabbuka bi'aad

Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?

Aya 7

إِرَمَ ذَاتِ ٱلْعِمَادِ

Iramaa zaatil 'imaad

Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.

Aya 8

ٱلَّتِى لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِى ٱلْبِلَٰدِ

Allatee lam yukhlaq misluhaa fil bilaad

Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).

Aya 9

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُوا۟ ٱلصَّخْرَ بِٱلْوَادِ

Wa samoodal lazeena jaabus sakhra bil waad

Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?

Aya 10

وَفِرْعَوْنَ ذِى ٱلْأَوْتَادِ

Wa fir'awna zil awtaad

Da Fir'auna mai turãku.

Aya 11

ٱلَّذِينَ طَغَوْا۟ فِى ٱلْبِلَٰدِ

Allazeena taghaw fil bilaad

Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?

Aya 12

فَأَكْثَرُوا۟ فِيهَا ٱلْفَسَادَ

Fa aksaroo feehal fasaad

Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.

Aya 13

فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ

Fasabba 'alaihim Rabbuka sawta 'azaab

Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.

Aya 14

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلْمِرْصَادِ

Inna Rabbaka labil mirsaad

Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

Aya 15

فَأَمَّا ٱلْإِنسَٰنُ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكْرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَكْرَمَنِ

Fa ammal insaanu izaa mab talaahu Rabbuhoo fa akramahoo wa na' 'amahoo fa yaqoolu Rabbeee akraman

To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."

Aya 16

وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَهَٰنَنِ

Wa ammaaa izaa mabtalaahu faqadara 'alaihi rizqahoo fa yaqoolu Rabbeee ahaanan

Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."

Aya 17

كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ ٱلْيَتِيمَ

Kalla bal laa tukrimooo nal yateem

A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!

Aya 18

وَلَا تَحَٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ

Wa laa tahaaaddoona 'alaata'aamil miskeen

Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!

Aya 19

وَتَأْكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكْلًۭا لَّمًّۭا

Wa taakuloonat turaasa aklal lammaa

Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.

Aya 20

وَتُحِبُّونَ ٱلْمَالَ حُبًّۭا جَمًّۭا

Wa tuhibboonal maala hubban jammaa

Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.

Aya 21

كَلَّآ إِذَا دُكَّتِ ٱلْأَرْضُ دَكًّۭا دَكًّۭا

Kallaaa izaaa dukkatil ardu dakkan dakka

A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.

Aya 22

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلْمَلَكُ صَفًّۭا صَفًّۭا

Wa jaaa'a Rabbuka wal malaku saffan saffaa

Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.

Aya 23

وَجِا۟ىٓءَ يَوْمَئِذٍۭ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍۢ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكْرَىٰ

Wa jeee'a yawma'izim bi jahannnam; Yawma 'iziny yatazakkarul insaanu wa annaa lahuz zikraa

Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!

Aya 24

يَقُولُ يَٰلَيْتَنِى قَدَّمْتُ لِحَيَاتِى

Yaqoolu yaa laitanee qaddamtu lihayaatee

Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"

Aya 25

فَيَوْمَئِذٍۢ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٌۭ

Fa Yawma izil laa yu'azzibu 'azaabahooo ahad

To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.

Aya 26

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٌۭ

Wa laa yoosiqu wasaaqa hooo ahad

Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.

Aya 27

يَٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفْسُ ٱلْمُطْمَئِنَّةُ

Yaaa ayyatuhan nafsul mutma 'innah

Yã kai rai mai natsuwa!

Aya 28

ٱرْجِعِىٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةًۭ مَّرْضِيَّةًۭ

Irji'eee ilaa Rabbiki raadiyatam mardiyyah

Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).

Aya 29

فَٱدْخُلِى فِى عِبَٰدِى

Fadkhulee fee 'ibaadee

Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).

Aya 30

وَٱدْخُلِى جَنَّتِى

Wadkhulee jannatee

Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).