Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Balad
90

Balad — Gari

البَلَدِ
Makkiyya Aya 20
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

لَآ أُقْسِمُ بِهَٰذَا ٱلْبَلَدِ

Laaa uqsimu bihaazal balad

Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.

Aya 2

وَأَنتَ حِلٌّۢ بِهَٰذَا ٱلْبَلَدِ

Wa anta hillum bihaazal balad

Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.

Aya 3

وَوَالِدٍۢ وَمَا وَلَدَ

Wa waalidinw wa maa walad

Da mahaifi da abin da ya haifa.

Aya 4

لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَٰنَ فِى كَبَدٍ

Laqad khalaqnal insaana fee kabad

Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.

Aya 5

أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌۭ

Ayahsabu al-lai yaqdira 'alaihi ahad

Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?

Aya 6

يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًۭا لُّبَدًا

Yaqoolu ahlaktu maalal lubadaa

Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"

Aya 7

أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ

Ayahsabu al lam yarahooo ahad

Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?

Aya 8

أَلَمْ نَجْعَل لَّهُۥ عَيْنَيْنِ

Alam naj'al lahoo 'aynayn

Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?

Aya 9

وَلِسَانًۭا وَشَفَتَيْنِ

Wa lisaananw wa shafatayn

Da harshe, da leɓɓa biyu.

Aya 10

وَهَدَيْنَٰهُ ٱلنَّجْدَيْنِ

Wa hadaynaahun najdayn

Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?

Aya 11

فَلَا ٱقْتَحَمَ ٱلْعَقَبَةَ

Falaq tahamal-'aqabah

To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?

Aya 12

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْعَقَبَةُ

Wa maaa adraaka mal'aqabah

Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?

Aya 13

فَكُّ رَقَبَةٍ

Fakku raqabah

Ita ce fansar wuyan bãwa.

Aya 14

أَوْ إِطْعَٰمٌۭ فِى يَوْمٍۢ ذِى مَسْغَبَةٍۢ

Aw it'aamun fee yawmin zee masghabah

Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.

Aya 15

يَتِيمًۭا ذَا مَقْرَبَةٍ

Yateeman zaa maqrabah

Ga marãya ma'abũcin zumunta.

Aya 16

أَوْ مِسْكِينًۭا ذَا مَتْرَبَةٍۢ

Aw miskeenan zaa matrabah

Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.

Aya 17

ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلْمَرْحَمَةِ

Summa kaana minal lazeena aamanoo wa tawaasaw bissabri wa tawaasaw bilmarhamah

Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.

Aya 18

أُو۟لَٰٓئِكَ أَصْحَٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ

Ulaaa'ika As-haabul maimanah

Waɗannan ne ma'abũta albarka

Aya 19

وَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ بِـَٔايَٰتِنَا هُمْ أَصْحَٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ

Wallazeena kafaroo bi aayaatinaa hum as-haabul Mash'amah

Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci

Aya 20

عَلَيْهِمْ نَارٌۭ مُّؤْصَدَةٌۢ

Alaihim naarum mu'sadah

A kansu akwai wata wuta abar kullewa.