Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Shams
91

Shams — Rana

الشَّمۡسِ
Makkiyya Aya 15
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَٱلشَّمْسِ وَضُحَىٰهَا

Wash shamsi wa duhaa haa

Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.

Aya 2

وَٱلْقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا

Wal qamari izaa talaa haa

Kuma da wata idan ya bi ta.

Aya 3

وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا

Wannahaari izaa jallaa haa

Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.

Aya 4

وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰهَا

Wallaili izaa yaghshaa haa

Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.

Aya 5

وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا

Wassamaaa'i wa maa banaahaa

Da sama da abin da ya gina ta.

Aya 6

وَٱلْأَرْضِ وَمَا طَحَىٰهَا

Wal ardi wa maa tahaahaa

Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.

Aya 7

وَنَفْسٍۢ وَمَا سَوَّىٰهَا

Wa nafsinw wa maa sawwaahaa

Da rai da abin da ya daidaita shi.

Aya 8

فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَىٰهَا

Fa-alhamahaa fujoorahaa wa taqwaahaa

Sa'an nan ya sanar da shi fãjircinsa da shiryuwarsa.

Aya 9

قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّىٰهَا

Qad aflaha man zakkaahaa

Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sãmi babban rabo.

Aya 10

وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا

Wa qad khaaba man dassaahaa

Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya tãɓe.

Aya 11

كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَىٰهَآ

Kazzabat Samoodu bi taghwaahaaa

Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.

Aya 12

إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشْقَىٰهَا

Izim ba'asa ashqaahaa

A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).

Aya 13

فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقْيَٰهَا

Faqaala lahum Rasoolul laahi naaqatal laahi wa suqiyaahaa

Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"

Aya 14

فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمْ فَسَوَّىٰهَا

Fakazzaboohu fa'aqaroohaa fadamdama 'alaihim Rabbuhum bizambihim fasaw waahaa

Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).

Aya 15

وَلَا يَخَافُ عُقْبَٰهَا

Wa laa yakhaafu'uqbaahaa

Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).