Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Lail
92

Lail — Dare

اللَّيۡلِ
Makkiyya Aya 21
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ

Wallaili izaa yaghshaa

Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.

Aya 2

وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ

Wannahaari izaa tajalla

Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.

Aya 3

وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰٓ

Wa maa khalaqaz zakara wal unthaa

Da abin da ya halitta namiji da mace.

Aya 4

إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ

Inna sa'yakum lashattaa

Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.

Aya 5

فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَٱتَّقَىٰ

Fa ammaa man a'taa wattaqaa

To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.

Aya 6

وَصَدَّقَ بِٱلْحُسْنَىٰ

Wa saddaqa bil husnaa

Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.

Aya 7

فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْيُسْرَىٰ

Fasanu yassiruhoo lilyusraa

To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.

Aya 8

وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسْتَغْنَىٰ

Wa ammaa mam bakhila wastaghnaa

Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.

Aya 9

وَكَذَّبَ بِٱلْحُسْنَىٰ

Wa kazzaba bil husnaa

Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.

Aya 10

فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْعُسْرَىٰ

Fasanu yassiruhoo lil'usraa

To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.

Aya 11

وَمَا يُغْنِى عَنْهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ

Wa maa yughnee 'anhu maaluhooo izaa taraddaa

Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).

Aya 12

إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ

Inna 'alainaa lal hudaa

Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.

Aya 13

وَإِنَّ لَنَا لَلْءَاخِرَةَ وَٱلْأُولَىٰ

Wa inna lanaa lal Aakhirata wal oolaa

Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.

Aya 14

فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًۭا تَلَظَّىٰ

Fa anzartukum naaran talazzaa

Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.

Aya 15

لَا يَصْلَىٰهَآ إِلَّا ٱلْأَشْقَى

Laa yaslaahaaa illal ashqaa

Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.

Aya 16

ٱلَّذِى كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ

Allazee kazzaba wa tawallaa

Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.

Aya 17

وَسَيُجَنَّبُهَا ٱلْأَتْقَى

Wa sa yujannnabuhal atqaa

Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.

Aya 18

ٱلَّذِى يُؤْتِى مَالَهُۥ يَتَزَكَّىٰ

Allazee yu'tee maalahoo yatazakkaa

Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.

Aya 19

وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُۥ مِن نِّعْمَةٍۢ تُجْزَىٰٓ

Wa maa li ahadin 'indahoo min ni'matin tujzaaa

Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.

Aya 20

إِلَّا ٱبْتِغَآءَ وَجْهِ رَبِّهِ ٱلْأَعْلَىٰ

Illab tighaaa'a wajhi rabbihil a 'laa

Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.

Aya 21

وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ

Wa lasawfa yardaa

To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).