وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ
Wallaili izaa yaghshaa
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ
Wallaili izaa yaghshaa
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ
Wannahaari izaa tajalla
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰٓ
Wa maa khalaqaz zakara wal unthaa
Da abin da ya halitta namiji da mace.
إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ
Inna sa'yakum lashattaa
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَٱتَّقَىٰ
Fa ammaa man a'taa wattaqaa
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
وَصَدَّقَ بِٱلْحُسْنَىٰ
Wa saddaqa bil husnaa
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْيُسْرَىٰ
Fasanu yassiruhoo lilyusraa
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسْتَغْنَىٰ
Wa ammaa mam bakhila wastaghnaa
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
وَكَذَّبَ بِٱلْحُسْنَىٰ
Wa kazzaba bil husnaa
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْعُسْرَىٰ
Fasanu yassiruhoo lil'usraa
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
وَمَا يُغْنِى عَنْهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ
Wa maa yughnee 'anhu maaluhooo izaa taraddaa
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ
Inna 'alainaa lal hudaa
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
وَإِنَّ لَنَا لَلْءَاخِرَةَ وَٱلْأُولَىٰ
Wa inna lanaa lal Aakhirata wal oolaa
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًۭا تَلَظَّىٰ
Fa anzartukum naaran talazzaa
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.
لَا يَصْلَىٰهَآ إِلَّا ٱلْأَشْقَى
Laa yaslaahaaa illal ashqaa
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.
ٱلَّذِى كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
Allazee kazzaba wa tawallaa
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.
وَسَيُجَنَّبُهَا ٱلْأَتْقَى
Wa sa yujannnabuhal atqaa
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.
ٱلَّذِى يُؤْتِى مَالَهُۥ يَتَزَكَّىٰ
Allazee yu'tee maalahoo yatazakkaa
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.
وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُۥ مِن نِّعْمَةٍۢ تُجْزَىٰٓ
Wa maa li ahadin 'indahoo min ni'matin tujzaaa
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.
إِلَّا ٱبْتِغَآءَ وَجْهِ رَبِّهِ ٱلْأَعْلَىٰ
Illab tighaaa'a wajhi rabbihil a 'laa
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.
وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ
Wa lasawfa yardaa
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).