Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Alaƙ
96

Alaƙ — Gudan Jini

العَلَقِ
Makkiyya Aya 19
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

ٱقْرَأْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلَّذِى خَلَقَ

Iqra bismi rab bikal lazee khalaq

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.

Aya 2

خَلَقَ ٱلْإِنسَٰنَ مِنْ عَلَقٍ

Khalaqal insaana min 'alaq

Ya hahitta mutum daga gudan jini.

Aya 3

ٱقْرَأْ وَرَبُّكَ ٱلْأَكْرَمُ

Iqra wa rab bukal akram

Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.

Aya 4

ٱلَّذِى عَلَّمَ بِٱلْقَلَمِ

Al lazee 'allama bil qalam

Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.

Aya 5

عَلَّمَ ٱلْإِنسَٰنَ مَا لَمْ يَعْلَمْ

'Al lamal insaana ma lam y'alam

Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.

Aya 6

كَلَّآ إِنَّ ٱلْإِنسَٰنَ لَيَطْغَىٰٓ

Kallaa innal insaana layatghaa

A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).

Aya 7

أَن رَّءَاهُ ٱسْتَغْنَىٰٓ

Ar-ra aahus taghnaa

Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.

Aya 8

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجْعَىٰٓ

Innna ilaa rabbikar ruj'aa

Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.

Aya 9

أَرَءَيْتَ ٱلَّذِى يَنْهَىٰ

Ara-aital lazee yanhaa

Shin, kã ga wanda ke hana.

Aya 10

عَبْدًا إِذَا صَلَّىٰٓ

'Abdan iza sallaa

Bãwã idan yã yi salla?

Aya 11

أَرَءَيْتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلْهُدَىٰٓ

Ara-aita in kana 'alal hudaa

Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?

Aya 12

أَوْ أَمَرَ بِٱلتَّقْوَىٰٓ

Au amara bit taqwaa

Ko ya yi umurni da taƙawa?

Aya 13

أَرَءَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ

Ara-aita in kaz zaba wa ta walla

Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?

Aya 14

أَلَمْ يَعْلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ

Alam y'alam bi-an nal lahaa yaraa

Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?

Aya 15

كَلَّا لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًۢا بِٱلنَّاصِيَةِ

Kalla la illam yantahi la nasfa'am bin nasiyah

A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.

Aya 16

نَاصِيَةٍۢ كَٰذِبَةٍ خَاطِئَةٍۢ

Nasiyatin kazi batin khaatiyah

Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.

Aya 17

فَلْيَدْعُ نَادِيَهُۥ

Fal yad'u naadiyah

Sai ya kirayi ƙungiyarsa.

Aya 18

سَنَدْعُ ٱلزَّبَانِيَةَ

Sanad 'uz zabaaniyah

Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).

Aya 19

كَلَّا لَا تُطِعْهُ وَٱسْجُدْ وَٱقْتَرِب ۩

Kalla; la tuti'hu wasjud waqtarib

A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).