Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Tin
95

Tin — Ɓaure

التِّينِ
Makkiyya Aya 8
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيْتُونِ

Wat teeni waz zaitoon

Inã rantsuwa da Attinu da Azzaitũn.

Aya 2

وَطُورِ سِينِينَ

Wa toori sineen

Da Dũr Sĩnĩna.

Aya 3

وَهَٰذَا ٱلْبَلَدِ ٱلْأَمِينِ

Wa haazal balad-il ameen

Da wannan gari amintacce.

Aya 4

لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَٰنَ فِىٓ أَحْسَنِ تَقْوِيمٍۢ

Laqad khalaqnal insaana fee ahsani taqweem

Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa.

Aya 5

ثُمَّ رَدَدْنَٰهُ أَسْفَلَ سَٰفِلِينَ

Thumma ra dad naahu asfala saafileen

Sa'an nan, Muka mayar da shi mafi ƙasƙantar masu rauni

Aya 6

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّٰلِحَٰتِ فَلَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۢ

Ill-lal lazeena aamanoo wa 'amilus saalihaati; falahum ajrun ghairu mamnoon

Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, saboda haka suna da sakamako wanda bã ya yankewa.

Aya 7

فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعْدُ بِٱلدِّينِ

Fama yu kaz zibuka b'adu bid deen

To, bãyan haka mẽ ya sanya ka ka ƙaryata sakamako (wanda za a yi a bãyan Tãshin ¡iyãma)?

Aya 8

أَلَيْسَ ٱللَّهُ بِأَحْكَمِ ٱلْحَٰكِمِينَ

Alai sal laahu bi-ahkamil haakimeen

Ashe Allah bã Shi ne Mafi mãsu hukunci kyãwon hukunci ba?