Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Buruj
85

Buruj — Taurari

البُرُوجِ
Makkiyya Aya 22
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلْبُرُوجِ

Wassamaaa'i zaatil burooj

Inã rantsuwa da sama mai taurãrin lissafin shekara.

Aya 2

وَٱلْيَوْمِ ٱلْمَوْعُودِ

Wal yawmil maw'ood

Da yinin da aka yi alkawarin zuwansa,

Aya 3

وَشَاهِدٍۢ وَمَشْهُودٍۢ

Wa shaahidinw wa mashhood

Da yini mai shaidu, da yini da ake halarta a cikinsa

Aya 4

قُتِلَ أَصْحَٰبُ ٱلْأُخْدُودِ

Qutila as haabul ukhdood

An la'ani mutãnen rãmi.

Aya 5

ٱلنَّارِ ذَاتِ ٱلْوَقُودِ

Annaari zaatil waqood

Wato wuta wadda aka hura.

Aya 6

إِذْ هُمْ عَلَيْهَا قُعُودٌۭ

Iz hum 'alaihaa qu'ood

A lõkacin da suke a kan (gefen) ta a zazzaune.

Aya 7

وَهُمْ عَلَىٰ مَا يَفْعَلُونَ بِٱلْمُؤْمِنِينَ شُهُودٌۭ

Wa hum 'alaa maa yaf'aloona bilmu 'mineena shuhood

Alhãli sũ, bisa ga abin da suke aikatãwa ga mũminai, sunã halarce.

Aya 8

وَمَا نَقَمُوا۟ مِنْهُمْ إِلَّآ أَن يُؤْمِنُوا۟ بِٱللَّهِ ٱلْعَزِيزِ ٱلْحَمِيدِ

Wa maa naqamoo minhum illaaa aiyu'minoo billaahil 'azeezil Hameed

Kuma ba su tuhumce su ba, fãce kawai domin sun yi ĩmãni da Allah Mabuwãyi, wanda ake gõdewa.

Aya 9

ٱلَّذِى لَهُۥ مُلْكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَىْءٍۢ شَهِيدٌ

Allazee lahoo mulkus samaawaati wal ard; wallaahu 'alaa kulli shai 'in Shaheed

Wanda Yake shi ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma Allah a kan kõme halarce Yake.

Aya 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُوا۟ ٱلْمُؤْمِنِينَ وَٱلْمُؤْمِنَٰتِ ثُمَّ لَمْ يَتُوبُوا۟ فَلَهُمْ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمْ عَذَابُ ٱلْحَرِيقِ

Innal lazeena fatanul mu'mineena wal mu'minaati summa lam yatooboo falahum 'azaabu Jahannama wa lahum 'azaabul hareeq

Lalle ne waɗanda suka fitini mũminai maza da mũminai mãta, sa'an nan ba su tũba ba to, sunã da azãbar Jahannama, kuma sunã da azãbar gõbara.

Aya 11

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّٰلِحَٰتِ لَهُمْ جَنَّٰتٌۭ تَجْرِى مِن تَحْتِهَا ٱلْأَنْهَٰرُ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْفَوْزُ ٱلْكَبِيرُ

Innal lazeena aamanoo wa 'amilus saalihaati lahum Jannaatun tajree min tahtihal anhaar; zaalikal fawzul kabeer

Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da gidãjen Aljanna, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashin gidãjen. Wancan abu fa shi ne rabo babba.

Aya 12

إِنَّ بَطْشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ

Inna batsha Rabbika lashadeed

Lalle ne damƙar Ubangijinka mai tsanani ce ƙwarai.

Aya 13

إِنَّهُۥ هُوَ يُبْدِئُ وَيُعِيدُ

Innahoo Huwa yubdi'u wa yu'eed

Lalle ne Shĩ, Shi ne Mai ƙãga halitta, kuma Ya mayar da ita (bãyan mutuwa).

Aya 14

وَهُوَ ٱلْغَفُورُ ٱلْوَدُودُ

Wa Huwal Ghafoorul Wadood

Kuma Shi ne Mai gãfara, Mai bayyana sõyayya.

Aya 15

ذُو ٱلْعَرْشِ ٱلْمَجِيدُ

Zul 'Arshil Majeed

Mai Al'arshi mai girma

Aya 16

فَعَّالٌۭ لِّمَا يُرِيدُ

Fa' 'aalul limaa yureed

Mai aikatãwa ga abin da Yake nufi.

Aya 17

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلْجُنُودِ

Hal ataaka hadeesul junood

Ko lãbãrin rundanõni yã zo maka.

Aya 18

فِرْعَوْنَ وَثَمُودَ

Fir'awna wa Samood

Fir'auna da samũdãwa?

Aya 19

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ فِى تَكْذِيبٍۢ

Balil lazeena kafaroo fee takzeeb

Ã'aha! waɗanda suka kãfirta sunã cikin ƙaryatãwa.

Aya 20

وَٱللَّهُ مِن وَرَآئِهِم مُّحِيطٌۢ

Wallaahu minw waraaa'ihim muheet

Alhãli, Allah daga bãyansu, Mai kẽwaye su ne (da saninSa).

Aya 21

بَلْ هُوَ قُرْءَانٌۭ مَّجِيدٌۭ

Bal huwa Quraanum Majeed

Ã'aha! Shi Alƙur'ãni ne mai girma.

Aya 22

فِى لَوْحٍۢ مَّحْفُوظٍۭ

Fee Lawhim Mahfooz

A cikin Allo tsararre.