Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Inshiƙaƙ
84

Inshiƙaƙ — Tsattsagewa

الانشِقَاقِ
Makkiyya Aya 25
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتْ

Izas samaaa'un shaqqat

Idan sama ta kẽce,

Aya 2

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ

Wa azinat li Rabbihaa wa huqqat

Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,

Aya 3

وَإِذَا ٱلْأَرْضُ مُدَّتْ

Wa izal ardu muddat

Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,

Aya 4

وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ

Wa alqat maa feehaa wa takhallat

Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.

Aya 5

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ

Wa azinat li Rabbihaa wa huqqat

Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,

Aya 6

يَٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًۭا فَمُلَٰقِيهِ

Yaaa ayyuhal insaanu innaka kaadihun ilaa Rabbika kad han famulaaqeeh

Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.

Aya 7

فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ

Fa ammaa man ootiya kitaabahoo biyameenih

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.

Aya 8

فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًۭا يَسِيرًۭا

Fasawfa yuhaasabu hi saabai yaseeraa

To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.

Aya 9

وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًۭا

Wa yanqalibu ilaaa ahlihee masrooraa

Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.

Aya 10

وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهْرِهِۦ

Wa ammaa man ootiya kitaabahoo waraaa'a zahrih

Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.

Aya 11

فَسَوْفَ يَدْعُوا۟ ثُبُورًۭا

Fasawfa yad'oo subooraa

To, zã shi dinga kiran halaka!

Aya 12

وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا

Wa yaslaa sa'eeraa

Kuma ya shiga sa'ĩr.

Aya 13

إِنَّهُۥ كَانَ فِىٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا

Innahoo kaana feee ahlihee masrooraa

Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.

Aya 14

إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ

Innahoo zanna al lai yahoor

Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.

Aya 15

بَلَىٰٓ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرًۭا

Balaaa inna Rabbahoo kaana bihee baseeraa

Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.

Aya 16

فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلشَّفَقِ

Falaaa uqsimu bishshafaq

To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.

Aya 17

وَٱلَّيْلِ وَمَا وَسَقَ

Wallaili wa maa wasaq

Da dare, da abin da ya ƙunsa.

Aya 18

وَٱلْقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ

Walqamari izat tasaq

Da watã idan (haskensa) ya cika.

Aya 19

لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍۢ

Latarkabunna tabaqan 'an tabaq

Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.

Aya 20

فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ

Famaa lahum laa yu'minoon

To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?

Aya 21

وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ ٱلْقُرْءَانُ لَا يَسْجُدُونَ ۩

Wa izaa quri'a 'alaihimul Quraanu laa yasjudoon

Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?

Aya 22

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ يُكَذِّبُونَ

Balil lazeena kafaroo yukazziboon

Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.

Aya 23

وَٱللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ

Wallaahu a'lamu bimaa yoo'oon

Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.

Aya 24

فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ

Fabashshirhum bi'azaabin aleem

Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.

Aya 25

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّٰلِحَٰتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۭ

Illal lazeena aamanoo wa 'amilus saalihaati lahum ajrun ghairu mamnoon

Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.