Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Muɗaffifin
83

Muɗaffifin — Masu Naƙasawa

المُطَفِّفِينَ
Makkiyya Aya 36
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَيْلٌۭ لِّلْمُطَفِّفِينَ

Wailul lil mutaffifeen

Bone ya tabbata ga mãsu naƙƙasãwa.

Aya 2

ٱلَّذِينَ إِذَا ٱكْتَالُوا۟ عَلَى ٱلنَّاسِ يَسْتَوْفُونَ

Allazeena izak taaloo 'alan naasi yastawfoon

Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu.

Aya 3

وَإِذَا كَالُوهُمْ أَو وَّزَنُوهُمْ يُخْسِرُونَ

Wa izaa kaaloohum aw wazanoohum yukhsiroon

Kuma idan sun auna musu da zakka ko da sikẽli, suna ragẽwa

Aya 4

أَلَا يَظُنُّ أُو۟لَٰٓئِكَ أَنَّهُم مَّبْعُوثُونَ

Alaa yazunnu ulaaa'ika annahum mab'oosoon

Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba?

Aya 5

لِيَوْمٍ عَظِيمٍۢ

Li Yawmin 'Azeem

Domin yini mai girma.

Aya 6

يَوْمَ يَقُومُ ٱلنَّاسُ لِرَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Yawma yaqoomun naasu li Rabbil 'aalameen

Yinin da mutãne ke tãshi zuwa ga Ubangijin halitta?

Aya 7

كَلَّآ إِنَّ كِتَٰبَ ٱلْفُجَّارِ لَفِى سِجِّينٍۢ

Kallaaa inna kitaabal fujjaari lafee Sijjeen

Haƙĩƙa lalle ne littãfin fãjirai dãhir, yana a cikin Sijjĩn.

Aya 8

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سِجِّينٌۭ

Wa maa adraaka maa Sijjeen

Kuma, mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽ wa Sijjĩn?

Aya 9

كِتَٰبٌۭ مَّرْقُومٌۭ

Kitaabum marqoom

Wani 1ittãfi ne rubũtacce.

Aya 10

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Wailuny yawma'izil lil mukazzibeen

Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.

Aya 11

ٱلَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ

Allazeena yukazziboona bi yawmid deen

Waɗanda suke ƙaryatãwa game da rãnar sakamako.

Aya 12

وَمَا يُكَذِّبُ بِهِۦٓ إِلَّا كُلُّ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ

Wa maa yukazzibu biheee illaa kullu mu'tadin aseem

Babũ mai ƙaryatãwa gare shi fãce dukan mai ƙẽtare haddi mai yawan zunubi.

Aya 13

إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ

Izaa tutlaa'alaihi aayaatunaa qaala asaateerul awwaleen

Idan ana karãtun ãyõyinmu, a kansa, sai ya ce: tãtsũniyõyin mutãnen farko ne.

Aya 14

كَلَّا ۖ بَلْ ۜ رَانَ عَلَىٰ قُلُوبِهِم مَّا كَانُوا۟ يَكْسِبُونَ

Kallaa bal raana 'alaa quloobihim maa kaanoo yaksiboon

A'aha! Bã haka ba, abin da suka kasance suna aikatãwa dai, yã yi tsãtsa a cikin zukãtãnsu.

Aya 15

كَلَّآ إِنَّهُمْ عَن رَّبِّهِمْ يَوْمَئِذٍۢ لَّمَحْجُوبُونَ

Kallaaa innahum 'ar Rabbihim yawma'izil lamah jooboon

A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne.

Aya 16

ثُمَّ إِنَّهُمْ لَصَالُوا۟ ٱلْجَحِيمِ

Summa innahum lasaa lul jaheem

Sa'an nan, lalle ne, sũ mãsu shiga cikin Jahĩm ne.

Aya 17

ثُمَّ يُقَالُ هَٰذَا ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ

Summa yuqaalu haazal lazee kuntum bihee tukazziboon

Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi."

Aya 18

كَلَّآ إِنَّ كِتَٰبَ ٱلْأَبْرَارِ لَفِى عِلِّيِّينَ

Kallaaa inna kitaabal abraari lafee'Illiyyeen

A'aha! Haƙĩƙa lalle ne littãfin mãsu ɗã'ã yana a cikin Illiyyĩna?

Aya 19

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا عِلِّيُّونَ

Wa maaa adraaka maa 'Illiyyoon

Kuma mẽne ne yã sanar da kai abin da ake cẽwa Illiyyũna?

Aya 20

كِتَٰبٌۭ مَّرْقُومٌۭ

Kitaabum marqoom

Wani littãfi ne rubũtacce.

Aya 21

يَشْهَدُهُ ٱلْمُقَرَّبُونَ

Yashhadu hul muqarra boon

Muƙarrabai suke halarta shi.

Aya 22

إِنَّ ٱلْأَبْرَارَ لَفِى نَعِيمٍ

Innal abraara lafee Na'eem

Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah tabbas suna cikin ni'ima.

Aya 23

عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ

'Alal araaa'iki yanzuroon

A kan karagu, suna ta kallo.

Aya 24

تَعْرِفُ فِى وُجُوهِهِمْ نَضْرَةَ ٱلنَّعِيمِ

Ta'rifu fee wujoohihim nadratan na'eem

Kana sani a cikin huskõkinsu, akwai kwarjinin ni'ima.

Aya 25

يُسْقَوْنَ مِن رَّحِيقٍۢ مَّخْتُومٍ

Yusqawna mir raheeqim makhtoom

Ana shãyar da sũ daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta.

Aya 26

خِتَٰمُهُۥ مِسْكٌۭ ۚ وَفِى ذَٰلِكَ فَلْيَتَنَافَسِ ٱلْمُتَنَٰفِسُونَ

Khitaamuhoo misk; wa fee zaalika falyatanaafasil Mutanaafisoon

¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, mãsu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nẽma.

Aya 27

وَمِزَاجُهُۥ مِن تَسْنِيمٍ

Wa mizaajuhoo min Tasneem

Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnĩm yake.

Aya 28

عَيْنًۭا يَشْرَبُ بِهَا ٱلْمُقَرَّبُونَ

'Ainaiy yashrabu bihal muqarraboon

(Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi.

Aya 29

إِنَّ ٱلَّذِينَ أَجْرَمُوا۟ كَانُوا۟ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ يَضْحَكُونَ

Innal lazeena ajramoo kaanoo minal lazeena aamanoo yadhakoon

Lalle ne, waɗanda suka kãfirta sun kasance (a dũniya) suna yi wa waɗanda suka yi ĩmãni dãriya.

Aya 30

وَإِذَا مَرُّوا۟ بِهِمْ يَتَغَامَزُونَ

Wa izaa marroo bihim yataghaamazoon

Kuma idan sun shuɗe su sai su dinga yin zunɗe.

Aya 31

وَإِذَا ٱنقَلَبُوٓا۟ إِلَىٰٓ أَهْلِهِمُ ٱنقَلَبُوا۟ فَكِهِينَ

Wa izan qalabooo ilaaa ahlihimun qalaboo fakiheen

Kuma idan suka jũya zuwa ga iyãlansu, sai su tafi suna kãkãci.

Aya 32

وَإِذَا رَأَوْهُمْ قَالُوٓا۟ إِنَّ هَٰٓؤُلَآءِ لَضَآلُّونَ

Wa izaa ra awhum qaalooo inna haaa'ulaaa'i ladaaal loon

Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne."

Aya 33

وَمَآ أُرْسِلُوا۟ عَلَيْهِمْ حَٰفِظِينَ

Wa maaa ursiloo 'alaihim haafizeen

Alhãli kuwa, ba a aike su ba dõmin su zama mãsu tsaro a kansu.

Aya 34

فَٱلْيَوْمَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ مِنَ ٱلْكُفَّارِ يَضْحَكُونَ

Fal yawmal lazeena aamanoo minal kuffaari yadhakoon

To, yau fa (a Lãhira] waɗanda suka yi ĩmãni, sũ ke yi wa kãfirai dãriya.

Aya 35

عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ

'Alal araaa'iki yanzuroon

A kan karagu, suna ta kallo.

Aya 36

هَلْ ثُوِّبَ ٱلْكُفَّارُ مَا كَانُوا۟ يَفْعَلُونَ

Hal suwwibal kuffaaru maa kaanoo yaf'aloon

Shin an sãka ma kãfirai abin da suka kasance suna aikatawa?