Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Infiɗar
82

Infiɗar — Tsagewa

الانفِطَارِ
Makkiyya Aya 19
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنفَطَرَتْ

Izas samaaa'un fatarat

Idan sama ta tsãge.

Aya 2

وَإِذَا ٱلْكَوَاكِبُ ٱنتَثَرَتْ

Wa izal kawaakibun tasarat

Kuma idan taurãri suka wãtse.

Aya 3

وَإِذَا ٱلْبِحَارُ فُجِّرَتْ

Wa izal bihaaru fujjirat

Kuma idan tẽkuna aka facce su.

Aya 4

وَإِذَا ٱلْقُبُورُ بُعْثِرَتْ

Wa izal qubooru bu'sirat

Kuma idan kaburbura aka tõne su.

Aya 5

عَلِمَتْ نَفْسٌۭ مَّا قَدَّمَتْ وَأَخَّرَتْ

'Alimat nafsum maa qaddamat wa akhkharat

Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.

Aya 6

يَٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَٰنُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ ٱلْكَرِيمِ

Yaaa ayyuhal insaaanu maa gharraka bi Rabbikal kareem

Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.

Aya 7

ٱلَّذِى خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ

Allazee khalaqaka fasaw waaka fa'adalak

Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.

Aya 8

فِىٓ أَىِّ صُورَةٍۢ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ

Feee ayye sooratim maa shaaa'a rakkabak

A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.

Aya 9

كَلَّا بَلْ تُكَذِّبُونَ بِٱلدِّينِ

Kalla bal tukazziboona bid deen

A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!

Aya 10

وَإِنَّ عَلَيْكُمْ لَحَٰفِظِينَ

Wa inna 'alaikum lahaa fizeen

Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.

Aya 11

كِرَامًۭا كَٰتِبِينَ

Kiraaman kaatibeen

Mãsu daraja, marubũta.

Aya 12

يَعْلَمُونَ مَا تَفْعَلُونَ

Ya'lamoona ma taf'aloon

Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.

Aya 13

إِنَّ ٱلْأَبْرَارَ لَفِى نَعِيمٍۢ

Innal abraara lafee na'eem

Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.

Aya 14

وَإِنَّ ٱلْفُجَّارَ لَفِى جَحِيمٍۢ

Wa innal fujjaara lafee jaheem

Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.

Aya 15

يَصْلَوْنَهَا يَوْمَ ٱلدِّينِ

Yaslawnahaa Yawmad Deen

Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.

Aya 16

وَمَا هُمْ عَنْهَا بِغَآئِبِينَ

Wa maa hum 'anhaa bighaaa 'ibeen

Bã zã su faku daga gare ta ba.

Aya 17

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلدِّينِ

Wa maaa adraaka maa Yawmud Deen

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako?

Aya 18

ثُمَّ مَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلدِّينِ

Summa maaa adraaka maa Yawmud Deen

Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?

Aya 19

يَوْمَ لَا تَمْلِكُ نَفْسٌۭ لِّنَفْسٍۢ شَيْـًۭٔا ۖ وَٱلْأَمْرُ يَوْمَئِذٍۢ لِّلَّهِ

Yawma laa tamliku nafsul linafsin shai'anw walamru yawma'izil lillaah

Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake.