Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Takwir
81

Takwir — Naɗewa

التَّكۡوِيرِ
Makkiyya Aya 29
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ

Izash shamsu kuwwirat

Idan rãna aka shafe haskenta

Aya 2

وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ

Wa izan nujoomun kadarat

Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

Aya 3

وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ

Wa izal jibaalu suyyirat

Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

Aya 4

وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ

Wa izal 'ishaaru 'uttilat

Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

Aya 5

وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ

Wa izal wuhooshu hushirat

Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

Aya 6

وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ

Wa izal bihaaru sujjirat

Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

Aya 7

وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ

Wa izan nufoosu zuwwijat

Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.

Aya 8

وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ

Wa izal maw'oodatu su'ilat

Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.

Aya 9

بِأَىِّ ذَنۢبٍۢ قُتِلَتْ

Bi ayyi zambin qutilat

"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

Aya 10

وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ

Wa izas suhufu nushirat

Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

Aya 11

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ

Wa izas samaaa'u kushitat

Kuma idan sama aka fẽɗe ta.

Aya 12

وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ

Wa izal jaheemu su'-'irat

Kuma idan Jahĩm aka hũra ta

Aya 13

وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ

Wa izal jannatu uzlifat

Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

Aya 14

عَلِمَتْ نَفْسٌۭ مَّآ أَحْضَرَتْ

'Alimat nafsum maaa ahdarat

Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

Aya 15

فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ

Falaaa uqsimu bil khunnas

To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.

Aya 16

ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ

Al jawaaril kunnas

Mãsu gudu suna ɓũya.

Aya 17

وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ

Wallaili izaa 'as'as

Da dare idan ya bãyar da bãya.

Aya 18

وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ

Wassubhi izaa tanaffas

Da sãfiya idan ta yi lumfashi.

Aya 19

إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍۢ كَرِيمٍۢ

Innahoo laqawlu rasoolin kareem

Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

Aya 20

ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍۢ

Zee quwwatin 'inda zil 'arshi makeen

Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

Aya 21

مُّطَاعٍۢ ثَمَّ أَمِينٍۢ

Mutaa'in samma ameen

Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

Aya 22

وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍۢ

Wa maa saahibukum bimajnoon

Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

Aya 23

وَلَقَدْ رَءَاهُ بِٱلْأُفُقِ ٱلْمُبِينِ

Wa laqad ra aahu bilufuqil mubeen

Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.

Aya 24

وَمَا هُوَ عَلَى ٱلْغَيْبِ بِضَنِينٍۢ

Wa maa huwa 'alal ghaibi bidaneen

Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.

Aya 25

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَٰنٍۢ رَّجِيمٍۢ

Wa maa huwa biqawli shaitaanir rajeem

Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

Aya 26

فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ

Fa ayna tazhaboon

Shin, a inã zã ku tafi?

Aya 27

إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌۭ لِّلْعَٰلَمِينَ

In huwa illaa zikrul lil'aalameen

Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

Aya 28

لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ

Liman shaaa'a minkum ai yastaqeem

Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

Aya 29

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Wa maa tashaaa'oona illaaa ai yashaaa 'al laahu Rabbul 'Aalameen

Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.