Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Abasa
80

Abasa — Ya Gintse Fuska

عَبَسَ
Makkiyya Aya 42
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ

'Abasa wa tawallaa.

Yã game huska kuma ya jũya bãya.

Aya 2

أَن جَآءَهُ ٱلْأَعْمَىٰ

An jaa-ahul 'a-maa

Sabõda makãho yã je masa.

Aya 3

وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ

Wa maa yudreeka la'allahu yaz zakkaa.

To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

Aya 4

أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكْرَىٰٓ

Au yaz zak karu fatanfa 'ahuz zikraa.

Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

Aya 5

أَمَّا مَنِ ٱسْتَغْنَىٰ

Amma manis taghnaa

Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

Aya 6

فَأَنتَ لَهُۥ تَصَدَّىٰ

Fa-anta lahu tasaddaa

Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

Aya 7

وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ

Wa ma 'alaika allaa yaz zakka.

To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

Aya 8

وَأَمَّا مَن جَآءَكَ يَسْعَىٰ

Wa amma man jaa-aka yas'a

Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

Aya 9

وَهُوَ يَخْشَىٰ

Wahuwa yakhshaa,

Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

Aya 10

فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ

Fa-anta 'anhu talah haa.

Kai kuma kã shagala ga barinsa!

Aya 11

كَلَّآ إِنَّهَا تَذْكِرَةٌۭ

Kalla innaha tazkirah

A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

Aya 12

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

Faman shaa a zakarah

Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

Aya 13

فِى صُحُفٍۢ مُّكَرَّمَةٍۢ

Fi suhufim mukar rama,

(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

Aya 14

مَّرْفُوعَةٍۢ مُّطَهَّرَةٍۭ

Marfoo'atim mutah hara,

Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

Aya 15

بِأَيْدِى سَفَرَةٍۢ

Bi'aidee safara

A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

Aya 16

كِرَامٍۭ بَرَرَةٍۢ

Kiraamim bararah.

Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

Aya 17

قُتِلَ ٱلْإِنسَٰنُ مَآ أَكْفَرَهُۥ

Qutilal-insanu maa akfarah.

An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

Aya 18

مِنْ أَىِّ شَىْءٍ خَلَقَهُۥ

Min aiyyi shai-in Khalaq

Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

Aya 19

مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ

Min nutfah; khalaqahu faqad-darah.

Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

Aya 20

ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ

Thummas sabeela yas-sarah

Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

Aya 21

ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقْبَرَهُۥ

Thumma amatahu fa-aqbarah

Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

Aya 22

ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ

Thumma iza shaa-a ansharah

Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

Aya 23

كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَآ أَمَرَهُۥ

Kalla lamma yaqdi maa amarah.

Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

Aya 24

فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَٰنُ إِلَىٰ طَعَامِهِۦٓ

Falyanzuril insanu ilaa ta-amih

To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

Aya 25

أَنَّا صَبَبْنَا ٱلْمَآءَ صَبًّۭا

Anna sabab nalmaa-a sabba.

Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

Aya 26

ثُمَّ شَقَقْنَا ٱلْأَرْضَ شَقًّۭا

Thumma sha qaqnal-arda shaqqa.

Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

Aya 27

فَأَنۢبَتْنَا فِيهَا حَبًّۭا

Fa ambatna feeha habba

Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

Aya 28

وَعِنَبًۭا وَقَضْبًۭا

Wa 'inabaw-wa qadba

Da inabi da ciyãwa.

Aya 29

وَزَيْتُونًۭا وَنَخْلًۭا

Wa zaitoonaw wanakh la'

Da zaitũni da itãcen dabĩno.

Aya 30

وَحَدَآئِقَ غُلْبًۭا

Wa hadaa-iqa ghulba

Da lambuna, mãsu yawan itãce.

Aya 31

وَفَٰكِهَةًۭ وَأَبًّۭا

Wa faki hataw-wa abba.

Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

Aya 32

مَّتَٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَٰمِكُمْ

Mata'al-lakum wa li-an'amikum.

Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

Aya 33

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ

Faiza jaa-atis saakhah.

To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

Aya 34

يَوْمَ يَفِرُّ ٱلْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ

Yauma yafir-rul mar-u min akheeh

Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

Aya 35

وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ

Wa ummihee wa abeeh

Da uwarsa da ubansa.

Aya 36

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ

Wa sahi batihee wa baneeh.

Da mãtarsa da ɗiyansa.

Aya 37

لِكُلِّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍۢ شَأْنٌۭ يُغْنِيهِ

Likul limri-im-minuhm yaumaa-izin shaa nuy-yughneeh

Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

Aya 38

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ مُّسْفِرَةٌۭ

Wujoo huny-yauma-izim-musfira;

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

Aya 39

ضَاحِكَةٌۭ مُّسْتَبْشِرَةٌۭ

Dahi katum mustab shirah

Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

Aya 40

وَوُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌۭ

Wa wujoohuy yauma-izin 'alaiha ghabar a

Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

Aya 41

تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ

Tarhaquha qatarah.

Baƙi zai rufe su.

Aya 42

أُو۟لَٰٓئِكَ هُمُ ٱلْكَفَرَةُ ٱلْفَجَرَةُ

Ulaa-ika humul-kafa ratul-fajarah.

Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).