Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Nazi'at
79

Nazi'at — Masu Fizga

النَّازِعَاتِ
Makkiyya Aya 46
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَٱلنَّٰزِعَٰتِ غَرْقًۭا

Wan naazi 'aati gharqa

Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

Aya 2

وَٱلنَّٰشِطَٰتِ نَشْطًۭا

Wan naa shi taati nashta

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

Aya 3

وَٱلسَّٰبِحَٰتِ سَبْحًۭا

Wass saabi-haati sabha

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

Aya 4

فَٱلسَّٰبِقَٰتِ سَبْقًۭا

Fass saabi qaati sabqa

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

Aya 5

فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًۭا

Fal mu dab-bi raati amra

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

Aya 6

يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ

Yawma tarjufur raajifa

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

Aya 7

تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ

Tatba'u har raadifa

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

Aya 8

قُلُوبٌۭ يَوْمَئِذٍۢ وَاجِفَةٌ

Quloobuny-yau maaiziw-waaji-fa

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

Aya 9

أَبْصَٰرُهَا خَٰشِعَةٌۭ

Absaa ruhaa khashi'ah

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

Aya 10

يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ

Ya qoo loona a-inna lamar doo doona fil haafirah

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

Aya 11

أَءِذَا كُنَّا عِظَٰمًۭا نَّخِرَةًۭ

Aizaa kunna 'izaa man-nakhirah

"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

Aya 12

قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًۭا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌۭ

Qaalu tilka izan karratun khaasirah.

Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

Aya 13

فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ

Fa inna ma hiya zajratuw-waahida

To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

Aya 14

فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ

Faizaa hum biss saahirah

Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

Aya 15

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ

Hal ataaka hadeethu Musaa

Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

Aya 16

إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى

Iz nadaahu rabbuhu bil waadil-muqad dasi tuwa

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

Aya 17

ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

Izhab ilaa fir'auna innahu taghaa.

Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

Aya 18

فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ

Faqul hal laka ilaa-an tazakka.

"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

Aya 19

وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ

Wa ahdi yaka ila rabbika fatakh sha

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

Aya 20

فَأَرَىٰهُ ٱلْءَايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ

Fa araahul-aayatal kubra.

Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.

Aya 21

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ

Fa kazzaba wa asaa.

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

Aya 22

ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ

Thumma adbara yas'aa.

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

Aya 23

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ

Fa hashara fanada.

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

Aya 24

فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ

Faqala ana rabbu kumul-a'laa.

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

Aya 25

فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْءَاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ

Fa-akha zahul laahu nakalal aakhirati wal-oola.

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

Aya 26

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةًۭ لِّمَن يَخْشَىٰٓ

Inna fee zaalika la'ibratal limaiy-yaksha

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

Aya 27

ءَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُ ۚ بَنَىٰهَا

A-antum a shaddu khalqan amis samaa-u banaaha.

Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

Aya 28

رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّىٰهَا

Raf'a sam kaha fasaw waaha

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

Aya 29

وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَىٰهَا

Wa aghtasha lailaha wa akhraja duhaaha.

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

Aya 30

وَٱلْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ

Wal arda b'ada zaalika dahaaha.

Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

Aya 31

أَخْرَجَ مِنْهَا مَآءَهَا وَمَرْعَىٰهَا

Akhraja minha maa-aha wa mar 'aaha.

Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

Aya 32

وَٱلْجِبَالَ أَرْسَىٰهَا

Wal jibala arsaaha.

Da duwatsu, Yã kafe ta.

Aya 33

مَتَٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَٰمِكُمْ

Mataa'al lakum wali an 'aamikum.

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

Aya 34

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلْكُبْرَىٰ

Fa-izaa jaaa'atit taaam matul kubraa.

To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

Aya 35

يَوْمَ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَٰنُ مَا سَعَىٰ

Yauma Yata zakkarul insaanu ma sa'aa.

Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

Aya 36

وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ

Wa burrizatil-jaheemu limany-yaraa.

Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

Aya 37

فَأَمَّا مَن طَغَىٰ

Fa ammaa man taghaa.

To, amma wanda ya yi girman kai.

Aya 38

وَءَاثَرَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا

Wa aasaral hayaatad dunyaa

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

Aya 39

فَإِنَّ ٱلْجَحِيمَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ

Fa innal jaheema hiyal maawaa.

To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

Aya 40

وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفْسَ عَنِ ٱلْهَوَىٰ

Wa ammaa man khaafa maqaama Rabbihee wa nahan nafsa 'anil hawaa

Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

Aya 41

فَإِنَّ ٱلْجَنَّةَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ

Fa innal jannata hiyal maawaa

To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

Aya 42

يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا

Yas'aloonaka 'anis saa'ati ayyaana mursaahaa

Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

Aya 43

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ

Feema anta min zikraahaa

Me ya haɗã ka da ambatonta?

Aya 44

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ

Ilaa Rabbika muntahaa haa

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

Aya 45

إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَىٰهَا

Innamaaa anta munziru maiy yakshaahaa

Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

Aya 46

كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوٓا۟ إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَىٰهَا

Ka annahum Yawma yarawnahaa lam yalbasooo illaa 'ashiyyatan aw duhaahaa

Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.