Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Naba'i
78

Naba'i — Labari

النَّبَإِ
Makkiyya Aya 40
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

عَمَّ يَتَسَآءَلُونَ

'Amma Yatasaa-aloon

A kan mẽ suke tambayar jũna?

Aya 2

عَنِ ٱلنَّبَإِ ٱلْعَظِيمِ

'Anin-nabaa-il 'azeem

A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur'ãni)?

Aya 3

ٱلَّذِى هُمْ فِيهِ مُخْتَلِفُونَ

Allazi hum feehi mukh talifoon

Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?

Aya 4

كَلَّا سَيَعْلَمُونَ

Kallaa sa y'alamoon

A'aha! Zã su sani.

Aya 5

ثُمَّ كَلَّا سَيَعْلَمُونَ

Thumma kallaa sa y'alamoon

Kuma, a'aha! Zã su sani.

Aya 6

أَلَمْ نَجْعَلِ ٱلْأَرْضَ مِهَٰدًۭا

Alam naj'alil arda mihaa da

Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?

Aya 7

وَٱلْجِبَالَ أَوْتَادًۭا

Wal jibaala au taada

Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?

Aya 8

وَخَلَقْنَٰكُمْ أَزْوَٰجًۭا

Wa khalaq naakum azwaaja

Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?

Aya 9

وَجَعَلْنَا نَوْمَكُمْ سُبَاتًۭا

Waja'alnan naumakum subata

Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?

Aya 10

وَجَعَلْنَا ٱلَّيْلَ لِبَاسًۭا

Waja'alnal laila libasa

Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?

Aya 11

وَجَعَلْنَا ٱلنَّهَارَ مَعَاشًۭا

Waja'alnan nahara ma 'aasha

Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?

Aya 12

وَبَنَيْنَا فَوْقَكُمْ سَبْعًۭا شِدَادًۭا

Wa banaina fauqakum sab 'an shi daada

Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?

Aya 13

وَجَعَلْنَا سِرَاجًۭا وَهَّاجًۭا

Waja'alna siraajaw wah haaja

Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?

Aya 14

وَأَنزَلْنَا مِنَ ٱلْمُعْصِرَٰتِ مَآءًۭ ثَجَّاجًۭا

Wa anzalna minal m'usiraati maa-an saj-jaaja

Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?

Aya 15

لِّنُخْرِجَ بِهِۦ حَبًّۭا وَنَبَاتًۭا

Linukh rija bihee habbaw wana baata

Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?

Aya 16

وَجَنَّٰتٍ أَلْفَافًا

Wa jan naatin alfafa

Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?

Aya 17

إِنَّ يَوْمَ ٱلْفَصْلِ كَانَ مِيقَٰتًۭا

Inna yaumal-fasli kana miqaata

Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.

Aya 18

يَوْمَ يُنفَخُ فِى ٱلصُّورِ فَتَأْتُونَ أَفْوَاجًۭا

Yauma yun fakhu fis-soori fataa toona afwaaja

Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.

Aya 19

وَفُتِحَتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ أَبْوَٰبًۭا

Wa futiha tis samaa-u fakaanat abwaaba

Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.

Aya 20

وَسُيِّرَتِ ٱلْجِبَالُ فَكَانَتْ سَرَابًا

Wa suyyi raatil jibaalu fa kaanat saraaba

Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.

Aya 21

إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتْ مِرْصَادًۭا

Inna jahan nama kaanat mirsaada

Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.

Aya 22

لِّلطَّٰغِينَ مَـَٔابًۭا

Lit taa gheena ma aaba

Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.

Aya 23

لَّٰبِثِينَ فِيهَآ أَحْقَابًۭا

Laa bitheena feehaa ahqaaba

Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.

Aya 24

لَّا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرْدًۭا وَلَا شَرَابًا

Laa ya zooqoona feeha bar daw walaa sharaaba

Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.

Aya 25

إِلَّا حَمِيمًۭا وَغَسَّاقًۭا

Illa hamee maw-wa ghas saaqa

Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.

Aya 26

جَزَآءًۭ وِفَاقًا

Jazaa-aw wi faaqa

Sakamako mai dãcẽwa.

Aya 27

إِنَّهُمْ كَانُوا۟ لَا يَرْجُونَ حِسَابًۭا

Innahum kaanu laa yarjoona hisaaba

Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.

Aya 28

وَكَذَّبُوا۟ بِـَٔايَٰتِنَا كِذَّابًۭا

Wa kazzabu bi aayaa tina kizzaba

Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyinMu, ƙaryatãwa!

Aya 29

وَكُلَّ شَىْءٍ أَحْصَيْنَٰهُ كِتَٰبًۭا

Wa kulla shai-in ahsai naahu kitaa ba

Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.

Aya 30

فَذُوقُوا۟ فَلَن نَّزِيدَكُمْ إِلَّا عَذَابًا

Fa zooqoo falan-nazee dakum ill-laa azaaba

Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.

Aya 31

إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ مَفَازًا

Inna lil mutta qeena mafaaza

Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.

Aya 32

حَدَآئِقَ وَأَعْنَٰبًۭا

Hadaa-iqa wa a'anaa ba

Lambuna da inabõbi.

Aya 33

وَكَوَاعِبَ أَتْرَابًۭا

Wa kaawa 'iba at raaba

Da cikakkun 'yammata, tsãrar jũna.

Aya 34

وَكَأْسًۭا دِهَاقًۭا

Wa ka'san di haaqa

Da hinjãlan giya cikakku.

Aya 35

لَّا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًۭا وَلَا كِذَّٰبًۭا

Laa yasma'oona fiha lagh waw walaa kizzaba

Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.

Aya 36

جَزَآءًۭ مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابًۭا

Jazaa-am mir-rabbika ataa-an hisaaba

Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.

Aya 37

رَّبِّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ٱلرَّحْمَٰنِ ۖ لَا يَمْلِكُونَ مِنْهُ خِطَابًۭا

Rabbis samaa waati wal ardi wa maa baina humar rahmaani laa yam likoona minhu khi taaba

Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.

Aya 38

يَوْمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلْمَلَٰٓئِكَةُ صَفًّۭا ۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنْ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحْمَٰنُ وَقَالَ صَوَابًۭا

Yauma yaqoo mur roohu wal malaa-ikatu saf-fal laa yata kalla moona illa man azina lahur rahmaanu wa qaala sawaaba

Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.

Aya 39

ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلْحَقُّ ۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ مَـَٔابًا

Zaalikal yaumul haqqu faman shaa-at ta khaaza ill-laa rabbihi ma-aaba

Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.

Aya 40

إِنَّآ أَنذَرْنَٰكُمْ عَذَابًۭا قَرِيبًۭا يَوْمَ يَنظُرُ ٱلْمَرْءُ مَا قَدَّمَتْ يَدَاهُ وَيَقُولُ ٱلْكَافِرُ يَٰلَيْتَنِى كُنتُ تُرَٰبًۢا

In naa anzar naakum azaaban qareebaiy-yauma yan zurul marr-u maa qaddamat yadaahu wa ya qoolul-kaafiru yaa lai tanee kuntu turaaba

Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"