Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Mursalat
77

Mursalat — Waɗanda Aka Aika

المُرۡسَلَاتِ
Makkiyya Aya 50
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَٱلْمُرْسَلَٰتِ عُرْفًۭا

Wal mursalaati'urfaa

Ina rantsuwa da iskõkin da ake sakõwa jẽre, sunã bin jũna.

Aya 2

فَٱلْعَٰصِفَٰتِ عَصْفًۭا

Fal'aasifaati 'asfaa

Sa'an nan, su zamã iskõki mãsu ƙarfi suna kaɗãwa da ƙarfi.

Aya 3

وَٱلنَّٰشِرَٰتِ نَشْرًۭا

Wannaashiraati nashraa

Kuma, mãsu watsa rahama wãtsãwa.

Aya 4

فَٱلْفَٰرِقَٰتِ فَرْقًۭا

Falfaariqaati farqaa

sa'an nan, da ãyõyi mãsu rarrabe gaskiya da ƙarya rarrabẽwa.

Aya 5

فَٱلْمُلْقِيَٰتِ ذِكْرًا

Falmulqiyaati zikra

Sa'an nan da malã'iku mãsu jẽfa tunãtarwa ga Manzanni.

Aya 6

عُذْرًا أَوْ نُذْرًا

'Uzran aw nuzraa

Domin yanke hamzari ko dõmin gargadi.

Aya 7

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَوَٰقِعٌۭ

Innamaa too'adoona lawaaqi'

Lalle ne, abin da ake yi muku wa'adi da shi tabbas mai aukuwa ne

Aya 8

فَإِذَا ٱلنُّجُومُ طُمِسَتْ

Fa izam nujoomu tumisat

To, idan taurãri aka shãfe haskensu.

Aya 9

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ فُرِجَتْ

Wa izas samaaa'u furijat

Kuma, idan sama aka tsãge ta.

Aya 10

وَإِذَا ٱلْجِبَالُ نُسِفَتْ

Wa izal jibaalu nusifat

Kuma, idan duwãtsu aka nike su.

Aya 11

وَإِذَا ٱلرُّسُلُ أُقِّتَتْ

Wa izar Rusulu uqqitat

Kuma, idan manzanni aka ƙayyade lõkacin tãra su.

Aya 12

لِأَىِّ يَوْمٍ أُجِّلَتْ

Li ayyi yawmin ujjilat

Domin babbar rãnar da aka yi wa ajali.

Aya 13

لِيَوْمِ ٱلْفَصْلِ

Li yawmil Fasl

Domin rãnar rarrabẽwa.

Aya 14

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ

Wa maaa adraaka maa yawmul fasl

Kuma, me ya sanar da kai rãnar rarrabẽwa?

Aya 15

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Wailuny yawma 'izillilmukazzibeen

Bone yã tabbata a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Aya 16

أَلَمْ نُهْلِكِ ٱلْأَوَّلِينَ

Alam nuhlikil awwaleen

Ashe, ba Mu halakar da (mãsu ƙaryatãw) na farko ba.

Aya 17

ثُمَّ نُتْبِعُهُمُ ٱلْءَاخِرِينَ

Summa nutbi'uhumul aakhireen

Sa'an nan, kuma zã Mu biyar musu da na ƙarshe?

Aya 18

كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِٱلْمُجْرِمِينَ

Kazzlika naf'alu bilmujrimeen

Haka nan, Muke aikatãwa da mãsu yin laifi.

Aya 19

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Wailunw yawma 'izil lil mukazzibeen

Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa!

Aya 20

أَلَمْ نَخْلُقكُّم مِّن مَّآءٍۢ مَّهِينٍۢ

Alam nakhlukkum mimmaaa'im maheen

Ashe, ba Mu halitta ku daga wani ruwa wulakantacce ba.

Aya 21

فَجَعَلْنَٰهُ فِى قَرَارٍۢ مَّكِينٍ

Faja'alnaahu fee qaraarim makeen

Sa'an nan Muka sanya shi a cikin wani wurin natsuwa amintacce.

Aya 22

إِلَىٰ قَدَرٍۢ مَّعْلُومٍۢ

Illaa qadrim ma'loom

Zuwa ga wani gwargwadon mudda sananna.

Aya 23

فَقَدَرْنَا فَنِعْمَ ٱلْقَٰدِرُونَ

Faqadarnaa fani'mal qaadiroon

Sa'an nan, Muka nũna iyãwarMu? Madalla da Mu, Mãsu nũna iyãwa.

Aya 24

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Wailuny yawma 'izil lilmukazzibeen

Bone ya tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa!

Aya 25

أَلَمْ نَجْعَلِ ٱلْأَرْضَ كِفَاتًا

Alam naj'alil arda kifaataa

Ashe, ba Mu sanya ƙasa matattarã ba.

Aya 26

أَحْيَآءًۭ وَأَمْوَٰتًۭا

Ahyaaa'anw wa amwaataa

Ga rãyayyu da matattu,

Aya 27

وَجَعَلْنَا فِيهَا رَوَٰسِىَ شَٰمِخَٰتٍۢ وَأَسْقَيْنَٰكُم مَّآءًۭ فُرَاتًۭا

Wa ja'alnaa feehaa rawaasiya shaamikhaatinw wa asqainaakum maaa'an furaataa

Kuma, Muka sanya, a cikinta, kafaffun duwãtsu maɗaukaka, kuma Muka shayar da ku ruwa mai dãɗi?

Aya 28

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Wailuny yawma 'izil lilmukazzibeen

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Aya 29

ٱنطَلِقُوٓا۟ إِلَىٰ مَا كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ

Intaliqooo ilaa maa kuntum bihee tukazziboon

Ku tafi zuwa ga abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi!

Aya 30

ٱنطَلِقُوٓا۟ إِلَىٰ ظِلٍّۢ ذِى ثَلَٰثِ شُعَبٍۢ

Intaliqooo ilaa zillin zee salaasi shu'ab

Ku tafi zuwa ga wata inuwa mai rassa uku.

Aya 31

لَّا ظَلِيلٍۢ وَلَا يُغْنِى مِنَ ٱللَّهَبِ

Laa zaleelinw wa laa yughnee minal lahab

Ita ba inuwar ba, kuma ba ta wadãtarwa daga harshen wuta.

Aya 32

إِنَّهَا تَرْمِى بِشَرَرٍۢ كَٱلْقَصْرِ

Innahaa tarmee bishararin kalqasr

Lalle ne, ita, tanã jifã da tartsatsi kamar sõraye.

Aya 33

كَأَنَّهُۥ جِمَٰلَتٌۭ صُفْرٌۭ

Ka annahoo jimaalatun sufr

Kamar dai su raƙumma ne baƙãƙe.

Aya 34

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Wailuny yawma 'izil lilmukazibeen

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Aya 35

هَٰذَا يَوْمُ لَا يَنطِقُونَ

Haazaa yawmu laa uantiqoon

Wannan, yini ne da bã zã su iya yin magana ba.

Aya 36

وَلَا يُؤْذَنُ لَهُمْ فَيَعْتَذِرُونَ

Wa laa yu'zanu lahum fa ya'taziroon

Bã zã a yi musu izni ba, balle su kãwo hanzari.

Aya 37

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Wailunw yawma 'izil lilmukazzibeen

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Aya 38

هَٰذَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ ۖ جَمَعْنَٰكُمْ وَٱلْأَوَّلِينَ

Haaza yawmul fasli jama 'naakum wal awwaleen

Wannan rãnar rarrabẽwa ce, Mun tattara ku tare da mutãnen farko.

Aya 39

فَإِن كَانَ لَكُمْ كَيْدٌۭ فَكِيدُونِ

Fa in kaana lakum kaidun fakeedoon

To, idan akwai wata dabara gare ku, sai ku yi ma Ni ita.

Aya 40

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Wailuny yawma'izil lilmukazzibeen

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Aya 41

إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى ظِلَٰلٍۢ وَعُيُونٍۢ

Innal muttaqeena fee zilaalinw wa 'uyoon

Lalle ne, mãsu taƙawa suna a cikin inuwõwi da marẽmari.

Aya 42

وَفَوَٰكِهَ مِمَّا يَشْتَهُونَ

Wa fawaakiha mimmaa yastahoon

Da wasu 'ya'yan itãce irin waɗanda suke marmari.

Aya 43

كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ

Kuloo washraboo haneee 'am bimaa kuntum ta'maloon

(A ce musu) "Ku ci ku sha cikin ni'ima sabõda abin da kuka kasance kuna aikatãwa."

Aya 44

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

Innaa kazaalika najzil muhsineen

Lalle ne, Mũ haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Aya 45

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Wailuny yawma 'izil lilmuzkazzibeen

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Aya 46

كُلُوا۟ وَتَمَتَّعُوا۟ قَلِيلًا إِنَّكُم مُّجْرِمُونَ

Kuloo wa tamatta'oo qaleelan innakum mujrimoon

(Ana ce musu) "Ku ci ku ji ɗan dãdi kaɗan, lalle ne dai ku mãsu laifi ne."

Aya 47

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Wailunny yawma 'izil lilmukazzibeen

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Aya 48

وَإِذَا قِيلَ لَهُمُ ٱرْكَعُوا۟ لَا يَرْكَعُونَ

Wa izaa qeela lahumur ka'oo aa yarka'oon

Kuma, idan an ce musu: "Ku yi rukũ'i; bã zã su yi rukũ'in (salla) ba."

Aya 49

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

Wailunny yawma 'izil lilmukazzibeen

Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

Aya 50

فَبِأَىِّ حَدِيثٍۭ بَعْدَهُۥ يُؤْمِنُونَ

Fabi ayyi hadeesim ba'dahoo yu'minoon

To, da wane lãbãri (Littãfi), waninsa (Alƙur'ãni) zã su yi ĩmãni