Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Haƙƙa
69

Haƙƙa — Mai Tabbata

الحَاقَّةِ
Makkiyya Aya 52
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

ٱلْحَآقَّةُ

Al haaaqqah

Kiran gaskiya!

Aya 2

مَا ٱلْحَآقَّةُ

Mal haaaqqah

Mẽne ne kiran gaskiya?

Aya 3

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْحَآقَّةُ

Wa maaa adraaka mal haaaqqah

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?

Aya 4

كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌۢ بِٱلْقَارِعَةِ

Kazzabat samoodu wa 'Aadum bil qaari'ah

Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!

Aya 5

فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا۟ بِٱلطَّاغِيَةِ

Fa-ammaa Samoodu fauhlikoo bittaaghiyah

To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.

Aya 6

وَأَمَّا عَادٌۭ فَأُهْلِكُوا۟ بِرِيحٍۢ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍۢ

Wa ammaa 'Aadun fa uhlikoo bireehin sarsarin 'aatiyah

Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.

Aya 7

سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍۢ وَثَمَٰنِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًۭا فَتَرَى ٱلْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍۢ

Sakhkharahaa 'alaihim sab'a la yaalinw wa samaaniyata ayyaamin husooman fataral qawma feehaa sar'aa ka annahum a'jaazu nakhlin khaawiyah

(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.

Aya 8

فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّنۢ بَاقِيَةٍۢ

Fahal taraa lahum mim baaqiyah

To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?

Aya 9

وَجَآءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُۥ وَٱلْمُؤْتَفِكَٰتُ بِٱلْخَاطِئَةِ

Wa jaaa'a Firawnu wa man qablahoo wal mu'tafikaatu bilhaati'ah

Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.

Aya 10

فَعَصَوْا۟ رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةًۭ رَّابِيَةً

Fa'ansaw Rasoola Rabbihim fa akhazahum akhzatar raabiyah

Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).

Aya 11

إِنَّا لَمَّا طَغَا ٱلْمَآءُ حَمَلْنَٰكُمْ فِى ٱلْجَارِيَةِ

Innaa lammaa taghal maaa'u hamalnaakum fil jaariyah

Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.

Aya 12

لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةًۭ وَتَعِيَهَآ أُذُنٌۭ وَٰعِيَةٌۭ

Linaj'alahaa lakum tazki ratanw-wa ta'iyahaa unzununw waa'iyah

Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).

Aya 13

فَإِذَا نُفِخَ فِى ٱلصُّورِ نَفْخَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ

Fa izaa nufikha fis soori nafkhatunw waahidah

To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.

Aya 14

وَحُمِلَتِ ٱلْأَرْضُ وَٱلْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةًۭ وَٰحِدَةًۭ

Wa humilatil ardu wal jibaalu fadukkataa dakkatanw waahidah

Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.

Aya 15

فَيَوْمَئِذٍۢ وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ

Fa yawma'izinw waqa'atil waaqi'ah

A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.

Aya 16

وَٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَهِىَ يَوْمَئِذٍۢ وَاهِيَةٌۭ

Wanshaqqatis samaaa'u fahiya yawma 'izinw-waahiyah

Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.

Aya 17

وَٱلْمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرْجَآئِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍۢ ثَمَٰنِيَةٌۭ

Wal malaku 'alaaa arjaaa'ihaa; wa yahmilu 'Arsha Rabbika fawqahum yawma'izin samaaniyah

Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.

Aya 18

يَوْمَئِذٍۢ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌۭ

Yawma'izin tu'radoona laa takhfaa min kum khaafiyah

A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.

Aya 19

فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَيَقُولُ هَآؤُمُ ٱقْرَءُوا۟ كِتَٰبِيَهْ

Fa ammaa man ootiya kitaabahoo biyameenihee fa yaqoolu haaa'umuq ra'oo kitaabiyah

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."

Aya 20

إِنِّى ظَنَنتُ أَنِّى مُلَٰقٍ حِسَابِيَهْ

Innee zannantu annee mulaaqin hisaabiyah

"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."

Aya 21

فَهُوَ فِى عِيشَةٍۢ رَّاضِيَةٍۢ

Fahuwa fee 'eeshatir raadiyah

Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.

Aya 22

فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍۢ

Fee jannnatin 'aaliyah

A cikin Aljanna maɗaukakiya.

Aya 23

قُطُوفُهَا دَانِيَةٌۭ

Qutoofuhaa daaniyah

Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),

Aya 24

كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَآ أَسْلَفْتُمْ فِى ٱلْأَيَّامِ ٱلْخَالِيَةِ

Kuloo washraboo haneee'am bimaaa aslaftum fil ayyaamil khaliyah

(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."

Aya 25

وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَٰلَيْتَنِى لَمْ أُوتَ كِتَٰبِيَهْ

Wa ammaa man ootiya kitaabahoo bishimaalihee fa yaqoolu yaalaitanee lam oota kitaaabiyah

Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"

Aya 26

وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ

Wa lam adri maa hisaabiyah

"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"

Aya 27

يَٰلَيْتَهَا كَانَتِ ٱلْقَاضِيَةَ

Yaa laitahaa kaanatil qaadiyah

"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!

Aya 28

مَآ أَغْنَىٰ عَنِّى مَالِيَهْ ۜ

Maaa aghnaa 'annee maaliyah

"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"

Aya 29

هَلَكَ عَنِّى سُلْطَٰنِيَهْ

Halaka 'annee sultaaniyah

"Ĩkona ya ɓace mini!"

Aya 30

خُذُوهُ فَغُلُّوهُ

Khuzoohu faghullooh

(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."

Aya 31

ثُمَّ ٱلْجَحِيمَ صَلُّوهُ

Summal Jaheema sallooh

"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."

Aya 32

ثُمَّ فِى سِلْسِلَةٍۢ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًۭا فَٱسْلُكُوهُ

Summa fee silsilatin zar'uhaa sab'oona ziraa'an faslukooh

"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."

Aya 33

إِنَّهُۥ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِٱللَّهِ ٱلْعَظِيمِ

Innahoo kaana laa yu'minubillaahil 'Azeem

"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"

Aya 34

وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ

wa laa yahuddu 'alaa ta'aamil miskeen

"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"

Aya 35

فَلَيْسَ لَهُ ٱلْيَوْمَ هَٰهُنَا حَمِيمٌۭ

Falaysa lahul yawma haahunaa hameem

"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."

Aya 36

وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍۢ

Wa laa ta'aamun illaa min ghisleen

"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."

Aya 37

لَّا يَأْكُلُهُۥٓ إِلَّا ٱلْخَٰطِـُٔونَ

Laa yaakuluhooo illal khati'oon

"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."

Aya 38

فَلَآ أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ

Falaaa uqsimu bimaa tubsiroon

To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,

Aya 39

وَمَا لَا تُبْصِرُونَ

Wa maa laa tubsiroon

Da abin da bã ku iya gani.

Aya 40

إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍۢ كَرِيمٍۢ

Innahoo laqawlu Rasoolin kareem

Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.

Aya 41

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍۢ ۚ قَلِيلًۭا مَّا تُؤْمِنُونَ

Wa ma huwa biqawli shaa'ir; qaleelam maa tu'minoon

Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.

Aya 42

وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍۢ ۚ قَلِيلًۭا مَّا تَذَكَّرُونَ

Wa laa biqawli kaahin; qaleelam maa tazakkaroon

Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.

Aya 43

تَنزِيلٌۭ مِّن رَّبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Tanzeelum mir rabbil 'aalameen

Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.

Aya 44

وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ ٱلْأَقَاوِيلِ

Wa law taqawwala 'alainaa ba'dal aqaaweel

Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.

Aya 45

لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِٱلْيَمِينِ

La-akhaznaa minhu bilyameen

Dã Mun kãma shi da dãma.

Aya 46

ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ ٱلْوَتِينَ

Summa laqata'naa minhul wateen

sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.

Aya 47

فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَٰجِزِينَ

Famaa minkum min ahadin'anhu haajizeen

Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.

Aya 48

وَإِنَّهُۥ لَتَذْكِرَةٌۭ لِّلْمُتَّقِينَ

Wa innahoo latazkiratul lilmuttaqeen

Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.

Aya 49

وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ

Wa inna lana'lamu anna minkum mukazzibeen

Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.

Aya 50

وَإِنَّهُۥ لَحَسْرَةٌ عَلَى ٱلْكَٰفِرِينَ

Wa innahu lahasratun 'alal kaafireen

Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.

Aya 51

وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلْيَقِينِ

Wa innahoo lahaqqul yaqeen

Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.

Aya 52

فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ

Fasbbih bismi Rabbikal 'Azeem

Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.