Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Ma'arij
70

Ma'arij — Matakala

المَعَارِجِ
Makkiyya Aya 44
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

سَأَلَ سَآئِلٌۢ بِعَذَابٍۢ وَاقِعٍۢ

Sa ala saaa'ilum bi'azaa binw-waaqi'

Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.

Aya 2

لِّلْكَٰفِرِينَ لَيْسَ لَهُۥ دَافِعٌۭ

Lilkaafireen laisa lahoo daafi'

Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.

Aya 3

مِّنَ ٱللَّهِ ذِى ٱلْمَعَارِجِ

Minal laahi zil ma'aarij

Daga Allah Mai matãkala.

Aya 4

تَعْرُجُ ٱلْمَلَٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيْهِ فِى يَوْمٍۢ كَانَ مِقْدَارُهُۥ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍۢ

Ta'rujul malaaa'ikatu war Roohu ilaihi fee yawmin kaana miqdaaruhoo khamseena alfa sanah

Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.

Aya 5

فَٱصْبِرْ صَبْرًۭا جَمِيلًا

Fasbir ssabran jameelaa

Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.

Aya 6

إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُۥ بَعِيدًۭا

Inaahum yarawnahoo ba'eedaa

Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.

Aya 7

وَنَرَىٰهُ قَرِيبًۭا

Wa naraahu qareebaa

Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.

Aya 8

يَوْمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلْمُهْلِ

Yawma takoonus samaaa'u kalmuhl

Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.

Aya 9

وَتَكُونُ ٱلْجِبَالُ كَٱلْعِهْنِ

Wa takoonul jibaalu kal'ihn

Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.

Aya 10

وَلَا يَسْـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمًۭا

Wa laa yas'alu hameemun hameemaa

Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.

Aya 11

يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ ٱلْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِى مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍۭ بِبَنِيهِ

Yubassaroonahum; ya waddul mujrimu law yaftadee min 'azaabi yawma'izim bibaneeh

Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,

Aya 12

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ

Wa saahibatihee wa akheeh

Da matarsa da ɗan'uwansa.

Aya 13

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِى تُـْٔوِيهِ

Wa faseelathil latee tu'weeh

Da danginsa, mãsu tattarã shi.

Aya 14

وَمَن فِى ٱلْأَرْضِ جَمِيعًۭا ثُمَّ يُنجِيهِ

Wa man fil ardi jamee'an summa yunjeeh

Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.

Aya 15

كَلَّآ ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

Kallaa innahaa lazaa

A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,

Aya 16

نَزَّاعَةًۭ لِّلشَّوَىٰ

Nazzaa'atal lishshawaa

Mai twãle fãtar goshi.

Aya 17

تَدْعُوا۟ مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ

Tad'oo man adbara wa tawallaa

Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.

Aya 18

وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰٓ

W jama'a fa aw'aa

Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.

Aya 19

۞ إِنَّ ٱلْإِنسَٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا

Innal insaana khuliqa haloo'aa

Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.

Aya 20

إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعًۭا

Izaa massahush sharru jazoo'aa

Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.

Aya 21

وَإِذَا مَسَّهُ ٱلْخَيْرُ مَنُوعًا

Wa izaa massahul khairu manoo'aa

Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.

Aya 22

إِلَّا ٱلْمُصَلِّينَ

Illal musalleen

Sai mãsu yin salla,

Aya 23

ٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَآئِمُونَ

Allazeena hum 'alaa Salaatihim daaa'imoon

Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.

Aya 24

وَٱلَّذِينَ فِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّۭ مَّعْلُومٌۭ

Wallazeena feee amwaalihim haqqum ma'loom

Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.

Aya 25

لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ

Lissaaa 'ili walmahroom

Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.

Aya 26

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ

Wallazeena yusaddiqoona bi yawmid Deen

Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.

Aya 27

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ

Wallazeena hum min 'azaabi Rabbihim mushfiqoon

Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.

Aya 28

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍۢ

Inna 'azaaba Rabbihim ghairu maamoon

Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.

Aya 29

وَٱلَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَٰفِظُونَ

Wallazeena hum lifuroo jihim haafizoon

Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.

Aya 30

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزْوَٰجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَٰنُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ

Illaa 'alaaa azwaajihim aw maa malakat aymaanuhum fainnahum ghairu maloomeen

Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.

Aya 31

فَمَنِ ٱبْتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُو۟لَٰٓئِكَ هُمُ ٱلْعَادُونَ

Famanib taghaa waraaa'a zaalika fa ulaaa'ika humul 'aadoon

To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.

Aya 32

وَٱلَّذِينَ هُمْ لِأَمَٰنَٰتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَٰعُونَ

Wallazeena hum li amaa naatihim wa 'ahdihim raa'oon

Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.

Aya 33

وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَٰدَٰتِهِمْ قَآئِمُونَ

Wallazeena hum bishahaadaatihim qaaa'imoon

Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.

Aya 34

وَٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ

Wallazeena hum 'alaa salaatihim yuhaafizoon

Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.

Aya 35

أُو۟لَٰٓئِكَ فِى جَنَّٰتٍۢ مُّكْرَمُونَ

Ulaaa'ika fee jannaatim mukramoon

Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne

Aya 36

فَمَالِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ

Famaa lil lazeena kafaroo qibalaka muhti'een

Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).

Aya 37

عَنِ ٱلْيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ عِزِينَ

'Anil yameeni wa 'anish shimaali 'izeen

Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!

Aya 38

أَيَطْمَعُ كُلُّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍۢ

Ayatma'u kullum ri'im minhum anyyudkhala jannata Na'eem

Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?

Aya 39

كَلَّآ ۖ إِنَّا خَلَقْنَٰهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ

Kallaaa innaa khalaq nahum mimmaa ya'lamoon

A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.

Aya 40

فَلَآ أُقْسِمُ بِرَبِّ ٱلْمَشَٰرِقِ وَٱلْمَغَٰرِبِ إِنَّا لَقَٰدِرُونَ

Falaaa uqsimu bi Rabbil mashaariqi wal maghaaribi innaa laqaadiroon

Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.

Aya 41

عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًۭا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ

'Alaaa an nubaddila khairam minhum wa maa Nahnu bimasbooqeen

Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.

Aya 42

فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا۟ وَيَلْعَبُوا۟ حَتَّىٰ يُلَٰقُوا۟ يَوْمَهُمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ

Fazarhum yakhoodoo wa yal'aboo hattaa yulaaqoo yaw mahumul lazee yoo'adoon

Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).

Aya 43

يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ سِرَاعًۭا كَأَنَّهُمْ إِلَىٰ نُصُبٍۢ يُوفِضُونَ

Yawma yakhrujoona minal ajdaasi siraa'an ka anna hum ilaa nusubiny yoofidoon

Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.

Aya 44

خَٰشِعَةً أَبْصَٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌۭ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلَّذِى كَانُوا۟ يُوعَدُونَ

Khaashi'atan absaaruhum tarhaquhum zillah; zaalikal yawmul lazee kaanoo yoo'adoon

Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)