Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Ƙalam
68

Ƙalam — Alƙalami

القَلَمِ
Makkiyya Aya 52
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

نٓ ۚ وَٱلْقَلَمِ وَمَا يَسْطُرُونَ

Noon; walqalami wa maa yasturoon

Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.

Aya 2

مَآ أَنتَ بِنِعْمَةِ رَبِّكَ بِمَجْنُونٍۢ

Maa anta bini'mati Rabbika bimajnoon

Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.

Aya 3

وَإِنَّ لَكَ لَأَجْرًا غَيْرَ مَمْنُونٍۢ

Wa inna laka la ajran ghaira mamnoon

Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.

Aya 4

وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٍۢ

Wa innaka la'alaa khuluqin 'azeem

Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.

Aya 5

فَسَتُبْصِرُ وَيُبْصِرُونَ

Fasatubsiru wa yubsiroon

Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.

Aya 6

بِأَييِّكُمُ ٱلْمَفْتُونُ

Bi ayyikumul maftoon

Ga wanenku haukã take.

Aya 7

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعْلَمُ بِٱلْمُهْتَدِينَ

Innaa Rabbaka Huwa a'lamu biman dalla 'an sabeelihee wa Huwa a'lamu bilmuhtadeen

Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.

Aya 8

فَلَا تُطِعِ ٱلْمُكَذِّبِينَ

Falaa tuti'il mukazzibeen

Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.

Aya 9

وَدُّوا۟ لَوْ تُدْهِنُ فَيُدْهِنُونَ

Waddoo law tudhinu fa-yudhinoon

Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.

Aya 10

وَلَا تُطِعْ كُلَّ حَلَّافٍۢ مَّهِينٍ

Wa laa tuti' kulla hallaa fim maheen

Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.

Aya 11

هَمَّازٍۢ مَّشَّآءٍۭ بِنَمِيمٍۢ

Hammaazim mash shaaa'im binameem

Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.

Aya 12

مَّنَّاعٍۢ لِّلْخَيْرِ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ

Mannaa'il lilkhairi mu'tadin aseem

Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.

Aya 13

عُتُلٍّۭ بَعْدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ

'Utullim ba'da zaalika zaneem

Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).

Aya 14

أَن كَانَ ذَا مَالٍۢ وَبَنِينَ

An kaana zaa maalinw-wa baneen

Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.

Aya 15

إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ

Izaa tutlaa 'alaihi aayaatunaa qaala asaateerul awwaleen

Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."

Aya 16

سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلْخُرْطُومِ

Sanasimuhoo 'alal khurtoom

Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.

Aya 17

إِنَّا بَلَوْنَٰهُمْ كَمَا بَلَوْنَآ أَصْحَٰبَ ٱلْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا۟ لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَ

Innaa balawnaahum kamaa balawnaaa As-haabal jannati iz 'aqsamoo la-yasri munnahaa musbiheen

Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.

Aya 18

وَلَا يَسْتَثْنُونَ

Wa laa yastasnoon

Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.

Aya 19

فَطَافَ عَلَيْهَا طَآئِفٌۭ مِّن رَّبِّكَ وَهُمْ نَآئِمُونَ

Fataafa 'alaihaa taaa'i fum mir rabbika wa hum naaa'imoon

Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.

Aya 20

فَأَصْبَحَتْ كَٱلصَّرِيمِ

Fa asbahat kassareem

Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.

Aya 21

فَتَنَادَوْا۟ مُصْبِحِينَ

Fatanaadaw musbiheen

Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.

Aya 22

أَنِ ٱغْدُوا۟ عَلَىٰ حَرْثِكُمْ إِن كُنتُمْ صَٰرِمِينَ

Anighdoo 'alaa harsikum in kuntum saarimeen

Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.

Aya 23

فَٱنطَلَقُوا۟ وَهُمْ يَتَخَٰفَتُونَ

Fantalaqoo wa hum yatakhaafatoon

Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).

Aya 24

أَن لَّا يَدْخُلَنَّهَا ٱلْيَوْمَ عَلَيْكُم مِّسْكِينٌۭ

Al laa yadkhulannahal yawma 'alaikum miskeen

"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"

Aya 25

وَغَدَوْا۟ عَلَىٰ حَرْدٍۢ قَٰدِرِينَ

Wa ghadaw 'alaa hardin qaadireen

Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.

Aya 26

فَلَمَّا رَأَوْهَا قَالُوٓا۟ إِنَّا لَضَآلُّونَ

Falammaa ra awhaa qaalooo innaa ladaaalloon

Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"

Aya 27

بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ

Bal nahnu mahroomoon

"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."

Aya 28

قَالَ أَوْسَطُهُمْ أَلَمْ أَقُل لَّكُمْ لَوْلَا تُسَبِّحُونَ

Qaala awsatuhum alam aqul lakum law laa tusabbihoon

Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"

Aya 29

قَالُوا۟ سُبْحَٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَٰلِمِينَ

Qaaloo subhaana rabbinaaa innaa kunnaa zaalimeen

Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."

Aya 30

فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَلَٰوَمُونَ

Fa aqbala ba'duhum 'alaa ba'diny yatalaawamoon

Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.

Aya 31

قَالُوا۟ يَٰوَيْلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَٰغِينَ

Qaaloo yaa wailanaaa innaa kunnaa taagheen

Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."

Aya 32

عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبْدِلَنَا خَيْرًۭا مِّنْهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ

'Asaa rabbunaaa any yubdilanaa khairam minhaaa innaaa ilaa rabbinaa raaghiboon

"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."

Aya 33

كَذَٰلِكَ ٱلْعَذَابُ ۖ وَلَعَذَابُ ٱلْءَاخِرَةِ أَكْبَرُ ۚ لَوْ كَانُوا۟ يَعْلَمُونَ

Kazaalikal azaab, wa la'azaabul aakhirati akbar; law kaanoo ya'lamoon

Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.

Aya 34

إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّٰتِ ٱلنَّعِيمِ

Inna lilmuttaqeena 'inda rabbihim jannaatin na'eem

Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.

Aya 35

أَفَنَجْعَلُ ٱلْمُسْلِمِينَ كَٱلْمُجْرِمِينَ

Afanaj'alul muslimeena kalmujrimeen

Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?

Aya 36

مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ

Maa lakum kaifa tahhkumoon

Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?

Aya 37

أَمْ لَكُمْ كِتَٰبٌۭ فِيهِ تَدْرُسُونَ

Am lakum kitaabun feehi tadrusoon

Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?

Aya 38

إِنَّ لَكُمْ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ

Inna lakum feehi lamaa takhaiyaroon

Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?

Aya 39

أَمْ لَكُمْ أَيْمَٰنٌ عَلَيْنَا بَٰلِغَةٌ إِلَىٰ يَوْمِ ٱلْقِيَٰمَةِ ۙ إِنَّ لَكُمْ لَمَا تَحْكُمُونَ

Am lakum aymaanun 'alainaa baalighatun ilaa yawmil qiyaamati inna lakum lamaa tahkumoon

Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?

Aya 40

سَلْهُمْ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ

Salhum ayyuhum bizaa lika za'eem

Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?

Aya 41

أَمْ لَهُمْ شُرَكَآءُ فَلْيَأْتُوا۟ بِشُرَكَآئِهِمْ إِن كَانُوا۟ صَٰدِقِينَ

Am lahum shurakaaa'u falyaatoo bishurakaaa 'ihim in kaanoo saadiqeen

Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.

Aya 42

يَوْمَ يُكْشَفُ عَن سَاقٍۢ وَيُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ فَلَا يَسْتَطِيعُونَ

Yawma yukshafu 'am saaqinw wa yud'awna ilas sujoodi falaa yastatee'oon

Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.

Aya 43

خَٰشِعَةً أَبْصَٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌۭ ۖ وَقَدْ كَانُوا۟ يُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ وَهُمْ سَٰلِمُونَ

Khaashi'atan absaaruhum tarhaquhum zillatunw wa qad kaanoo yud'awna ilassujoodi wa hum saalimoon

Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).

Aya 44

فَذَرْنِى وَمَن يُكَذِّبُ بِهَٰذَا ٱلْحَدِيثِ ۖ سَنَسْتَدْرِجُهُم مِّنْ حَيْثُ لَا يَعْلَمُونَ

Fazarnee wa many yukazzibu bihaazal hadeesi sanastad rijuhum min haisu laa ya'lamoon

Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.

Aya 45

وَأُمْلِى لَهُمْ ۚ إِنَّ كَيْدِى مَتِينٌ

Wa umlee lahum; inna kaidee mateen

Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.

Aya 46

أَمْ تَسْـَٔلُهُمْ أَجْرًۭا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍۢ مُّثْقَلُونَ

Am tas'aluhum ajran fahum mim maghramim musqaloon

Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?

Aya 47

أَمْ عِندَهُمُ ٱلْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ

Am 'indahumul ghaibu fahum yaktuboon

Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?

Aya 48

فَٱصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلْحُوتِ إِذْ نَادَىٰ وَهُوَ مَكْظُومٌۭ

Fasbir lihkmi rabbika wa laa takun kasaahibil boot; iz naadaa wa huwa makzoom

Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.

Aya 49

لَّوْلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعْمَةٌۭ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلْعَرَآءِ وَهُوَ مَذْمُومٌۭ

Law laaa an tadaara kahoo ni'matum mir rabbihee lanubiza bil'araaa'i wa huwa mazmoom

Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.

Aya 50

فَٱجْتَبَٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّٰلِحِينَ

Fajtabaahu rabbuhoo faja'alahoo minas saaliheen

Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.

Aya 51

وَإِن يَكَادُ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لَيُزْلِقُونَكَ بِأَبْصَٰرِهِمْ لَمَّا سَمِعُوا۟ ٱلذِّكْرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُۥ لَمَجْنُونٌۭ

Wa iny-yakaadul lazeena kafaroo la-yuzliqoonaka biabsaarihim lammaa saml'uz-Zikra wa yaqooloona innahoo lamajnoon

Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"

Aya 52

وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكْرٌۭ لِّلْعَٰلَمِينَ

Wa maa huwa illaa zikrul lil'aalameen

Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.