Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Ƙiyama
75

Ƙiyama — Tashin Ƙiyama

القِيَامَةِ
Makkiyya Aya 40
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

لَآ أُقْسِمُ بِيَوْمِ ٱلْقِيَٰمَةِ

Laaa uqsimu bi yawmil qiyaamah

Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.

Aya 2

وَلَآ أُقْسِمُ بِٱلنَّفْسِ ٱللَّوَّامَةِ

Wa laaa uqsimu bin nafsil lawwaamah

Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.

Aya 3

أَيَحْسَبُ ٱلْإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجْمَعَ عِظَامَهُۥ

Ayahsabul insaanu al lan najm'a 'izaamah

Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?

Aya 4

بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّىَ بَنَانَهُۥ

Balaa qaadireena 'alaaa an nusawwiya banaanah

Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.

Aya 5

بَلْ يُرِيدُ ٱلْإِنسَٰنُ لِيَفْجُرَ أَمَامَهُۥ

Bal yureedul insaanu liyafjura amaamah

Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.

Aya 6

يَسْـَٔلُ أَيَّانَ يَوْمُ ٱلْقِيَٰمَةِ

Yas'alu ayyyaana yawmul qiyaamah

Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"

Aya 7

فَإِذَا بَرِقَ ٱلْبَصَرُ

Fa izaa bariqal basar

To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).

Aya 8

وَخَسَفَ ٱلْقَمَرُ

We khasafal qamar

Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).

Aya 9

وَجُمِعَ ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ

Wa jumi'ash shamusu wal qamar

Aka tãra rãnã da watã

Aya 10

يَقُولُ ٱلْإِنسَٰنُ يَوْمَئِذٍ أَيْنَ ٱلْمَفَرُّ

Yaqoolul insaanu yaw ma 'izin aynal mafarr

Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"

Aya 11

كَلَّا لَا وَزَرَ

Kallaa laa wazar

A'aha! bãbu mafaka.

Aya 12

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ ٱلْمُسْتَقَرُّ

Ilaa rabbika yawma 'izinil mustaqarr

zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.

Aya 13

يُنَبَّؤُا۟ ٱلْإِنسَٰنُ يَوْمَئِذٍۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ

Yunabba 'ul insaanu yawma 'izim bimaa qaddama wa akhkhar

Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.

Aya 14

بَلِ ٱلْإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفْسِهِۦ بَصِيرَةٌۭ

Balil insaanu 'alaa nafsihee baseerah

Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.

Aya 15

وَلَوْ أَلْقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ

Wa law alqaa ma'aazeerah

Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).

Aya 16

لَا تُحَرِّكْ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعْجَلَ بِهِۦٓ

Laa tuharrik bihee lisaa naka lita'jala bih

Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).

Aya 17

إِنَّ عَلَيْنَا جَمْعَهُۥ وَقُرْءَانَهُۥ

Inna 'alainaa jam'ahoo wa qur aanah

Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.

Aya 18

فَإِذَا قَرَأْنَٰهُ فَٱتَّبِعْ قُرْءَانَهُۥ

Fa izaa qaraanaahu fattabi' qur aanah

To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.

Aya 19

ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا بَيَانَهُۥ

Summa inna 'alainaa bayaanah

sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.

Aya 20

كَلَّا بَلْ تُحِبُّونَ ٱلْعَاجِلَةَ

Kallaa bal tuhibboonal 'aajilah

A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.

Aya 21

وَتَذَرُونَ ٱلْءَاخِرَةَ

Wa tazaroonal Aakhirah

Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).

Aya 22

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ نَّاضِرَةٌ

Wujoohuny yawma 'izin naadirah

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.

Aya 23

إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٌۭ

Ilaa rabbihaa naazirah

Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.

Aya 24

وَوُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۭ بَاسِرَةٌۭ

Wa wujoohuny yawma 'izim baasirah

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.

Aya 25

تَظُنُّ أَن يُفْعَلَ بِهَا فَاقِرَةٌۭ

Tazunnu any yuf'ala bihaa faaqirah

Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.

Aya 26

كَلَّآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلتَّرَاقِىَ

Kallaaa izaa balaghatit taraaqee

A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.

Aya 27

وَقِيلَ مَنْ ۜ رَاقٍۢ

Wa qeela man raaq

kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"

Aya 28

وَظَنَّ أَنَّهُ ٱلْفِرَاقُ

Wa zanna annahul firaaq

Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.

Aya 29

وَٱلْتَفَّتِ ٱلسَّاقُ بِٱلسَّاقِ

Waltaffatis saaqu bissaaq

Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.

Aya 30

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ ٱلْمَسَاقُ

Ilaa rabbika yawma'izinil masaaq

Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.

Aya 31

فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ

Falaa saddaqa wa laa sallaa

To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!

Aya 32

وَلَٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ

Wa laakin kazzaba wa tawalla

Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!

Aya 33

ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ يَتَمَطَّىٰٓ

Summa zahaba ilaaa ahlihee yatamatta

Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.

Aya 34

أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ

Awlaa laka fa awlaa

Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.

Aya 35

ثُمَّ أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰٓ

Summa awlaa laka fa awla

Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.

Aya 36

أَيَحْسَبُ ٱلْإِنسَٰنُ أَن يُتْرَكَ سُدًى

Ayahsabul insaanu anyytraka sudaa

Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?

Aya 37

أَلَمْ يَكُ نُطْفَةًۭ مِّن مَّنِىٍّۢ يُمْنَىٰ

Alam yaku nutfatam mim maniyyiny yumnaa

Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)

Aya 38

ثُمَّ كَانَ عَلَقَةًۭ فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ

Summa kaana 'alaqata fakhalaq fasawwaa

Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;

Aya 39

فَجَعَلَ مِنْهُ ٱلزَّوْجَيْنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰٓ

Faja'ala minhuz zawjayniz zakara wal unsaa

Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?

Aya 40

أَلَيْسَ ذَٰلِكَ بِقَٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يُحْۦِىَ ٱلْمَوْتَىٰ

Alaisa zaalika biqaadirin 'alaaa any yuhyiyal mawtaa

Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?