Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Muddassir
74

Muddassir — Mai Rufa

المُدَّثِّرِ
Makkiyya Aya 56
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

يَٰٓأَيُّهَا ٱلْمُدَّثِّرُ

Yaaa ayyuhal muddassir

Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.

Aya 2

قُمْ فَأَنذِرْ

Qum fa anzir

Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi

Aya 3

وَرَبَّكَ فَكَبِّرْ

Wa rabbaka fakabbir

Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,

Aya 4

وَثِيَابَكَ فَطَهِّرْ

Wa siyaabaka fatahhir

Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,

Aya 5

وَٱلرُّجْزَ فَٱهْجُرْ

Warrujza fahjur

Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.

Aya 6

وَلَا تَمْنُن تَسْتَكْثِرُ

Wa laa tamnun tastaksir

Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri

Aya 7

وَلِرَبِّكَ فَٱصْبِرْ

Wa li Rabbika fasbir

Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure

Aya 8

فَإِذَا نُقِرَ فِى ٱلنَّاقُورِ

Fa izaa nuqira fin naaqoor

To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.

Aya 9

فَذَٰلِكَ يَوْمَئِذٍۢ يَوْمٌ عَسِيرٌ

Fazaalika yawma 'iziny yawmun 'aseer

To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya

Aya 10

عَلَى ٱلْكَٰفِرِينَ غَيْرُ يَسِيرٍۢ

'Alal kaafireena ghayru yaseer

A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.

Aya 11

ذَرْنِى وَمَنْ خَلَقْتُ وَحِيدًۭا

Zamee wa man khalaqtu waheedaa

Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,

Aya 12

وَجَعَلْتُ لَهُۥ مَالًۭا مَّمْدُودًۭا

Wa ja'altu lahoo maalam mamdoodaa

Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya

Aya 13

وَبَنِينَ شُهُودًۭا

Wa baneena shuhoodaa

Da ɗiyã halartattu,

Aya 14

وَمَهَّدتُّ لَهُۥ تَمْهِيدًۭا

Wa mahhattu lahoo tamheeda

Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.

Aya 15

ثُمَّ يَطْمَعُ أَنْ أَزِيدَ

Summa yat ma'u an azeed

Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!

Aya 16

كَلَّآ ۖ إِنَّهُۥ كَانَ لِءَايَٰتِنَا عَنِيدًۭا

Kallaaa innahoo kaana li Aayaatinaa 'aneedaa

Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyinMu, mai tsaurin kai.

Aya 17

سَأُرْهِقُهُۥ صَعُودًا

Sa urhiquhoo sa'oodaa

Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.

Aya 18

إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ

Innahoo fakkara wa qaddar

Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)

Aya 19

فَقُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ

Faqutila kayfa qaddar

Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.

Aya 20

ثُمَّ قُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ

Summa qutila kaifa qaddar

Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.

Aya 21

ثُمَّ نَظَرَ

Summa nazar

Sa'an nan, ya yi tunãni

Aya 22

ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ

Summa 'abasa wa basar

Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.

Aya 23

ثُمَّ أَدْبَرَ وَٱسْتَكْبَرَ

Summaa adbara wastakbar

Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,

Aya 24

فَقَالَ إِنْ هَٰذَآ إِلَّا سِحْرٌۭ يُؤْثَرُ

Faqaala in haazaaa illaa sihruny yu'sar

Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."

Aya 25

إِنْ هَٰذَآ إِلَّا قَوْلُ ٱلْبَشَرِ

In haazaaa illaa qawlul bashar

"Wannan maganar mutum dai ce."

Aya 26

سَأُصْلِيهِ سَقَرَ

Sa usleehi saqar

Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.

Aya 27

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سَقَرُ

Wa maaa adraaka maa saqar

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!

Aya 28

لَا تُبْقِى وَلَا تَذَرُ

Laa tubqee wa laa tazar

Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.

Aya 29

لَوَّاحَةٌۭ لِّلْبَشَرِ

Lawwaahatul lilbashar

Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).

Aya 30

عَلَيْهَا تِسْعَةَ عَشَرَ

'Alaihaa tis'ata 'ashar

A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.

Aya 31

وَمَا جَعَلْنَآ أَصْحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَٰٓئِكَةًۭ ۙ وَمَا جَعَلْنَا عِدَّتَهُمْ إِلَّا فِتْنَةًۭ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لِيَسْتَيْقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَٰبَ وَيَزْدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓا۟ إِيمَٰنًۭا ۙ وَلَا يَرْتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَٰبَ وَٱلْمُؤْمِنُونَ ۙ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِى قُلُوبِهِم مَّرَضٌۭ وَٱلْكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلًۭا ۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهْدِى مَن يَشَآءُ ۚ وَمَا يَعْلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَ ۚ وَمَا هِىَ إِلَّا ذِكْرَىٰ لِلْبَشَرِ

Wa maaja''alnaaa As haaban naari illaa malaaa 'ikatanw wa maa ja'alnaa 'iddatahum illaa fitnatal lillazeena kafaroo liyastayqinal lazeena ootul kitaaba wa yazdaadal lazeena aamanooo eemaananw wa laa yartaabal lazeena ootul kitaaba walmu'minoona wa liyaqoolal lazeena fee quloo bihim maradunw walkaafiroona maazaaa araadal laahu bihaazaa masalaa; kazaalika yudillul laahu many yashaaa'u wa yahdee many yashaaa'; wa maa ya'lamu junooda rabbika illaa hoo; wa maa hiya illaa zikraa lil bashar

Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.

Aya 32

كَلَّا وَٱلْقَمَرِ

Kallaa walqamar

A'aha! Ina rantsuwa da watã.

Aya 33

وَٱلَّيْلِ إِذْ أَدْبَرَ

Wallaili adbar

Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.

Aya 34

وَٱلصُّبْحِ إِذَآ أَسْفَرَ

Wassub hi izaaa asfar

Da sãfiya idan ta wãye.

Aya 35

إِنَّهَا لَإِحْدَى ٱلْكُبَرِ

Innahaa la ihdal kubar

Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.

Aya 36

نَذِيرًۭا لِّلْبَشَرِ

Nazeeral lilbashar

Mai gargaɗĩ ce ga mutum.

Aya 37

لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَتَقَدَّمَ أَوْ يَتَأَخَّرَ

Liman shaaa'a minkum any yataqaddama aw yata akhkhar

Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.

Aya 38

كُلُّ نَفْسٍۭ بِمَا كَسَبَتْ رَهِينَةٌ

Kullu nafsim bim kasabat raheenah

Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.

Aya 39

إِلَّآ أَصْحَٰبَ ٱلْيَمِينِ

Illaaa as haabal yameen

Fãce mutãnen dãma.

Aya 40

فِى جَنَّٰتٍۢ يَتَسَآءَلُونَ

Fee jannaatiny yata saaa'aloon

A cikin Aljanna suna tambayar jũna.

Aya 41

عَنِ ٱلْمُجْرِمِينَ

'Anil mujrimeen

Game da mãsu laifi.

Aya 42

مَا سَلَكَكُمْ فِى سَقَرَ

Maa salakakum fee saqar

(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"

Aya 43

قَالُوا۟ لَمْ نَكُ مِنَ ٱلْمُصَلِّينَ

Qaaloo lam naku minal musalleen

Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."

Aya 44

وَلَمْ نَكُ نُطْعِمُ ٱلْمِسْكِينَ

Wa lam naku nut'imul miskeen

"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."

Aya 45

وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلْخَآئِضِينَ

Wa kunnaa nakhoodu ma'al khaaa'ideen

"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."

Aya 46

وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ

Wa kunnaa nukazzibu bi yawmid Deen

"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."

Aya 47

حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلْيَقِينُ

Hattaaa ataanal yaqeen

"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."

Aya 48

فَمَا تَنفَعُهُمْ شَفَٰعَةُ ٱلشَّٰفِعِينَ

Famaa tanfa'uhum shafaa'atush shaafi'een

Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.

Aya 49

فَمَا لَهُمْ عَنِ ٱلتَّذْكِرَةِ مُعْرِضِينَ

Famaa lahum 'anittazkirati mu'rideen

Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.

Aya 50

كَأَنَّهُمْ حُمُرٌۭ مُّسْتَنفِرَةٌۭ

Ka annahum humurum mustanfirah

Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.

Aya 51

فَرَّتْ مِن قَسْوَرَةٍۭ

Farrat min qaswarah

Sun gudu daga zãki.

Aya 52

بَلْ يُرِيدُ كُلُّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ أَن يُؤْتَىٰ صُحُفًۭا مُّنَشَّرَةًۭ

Bal yureedu kullum ri'im minhum any yu'taa suhufam munashsharah

A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa

Aya 53

كَلَّا ۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلْءَاخِرَةَ

Kallaa bal laa yakhaafoonal aakhirah

A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.

Aya 54

كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذْكِرَةٌۭ

Kallaaa innahoo tazkirah

A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.

Aya 55

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

Fa man shaaa'a zakarah

Dõmin wanda ya so, ya tuna.

Aya 56

وَمَا يَذْكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ ۚ هُوَ أَهْلُ ٱلتَّقْوَىٰ وَأَهْلُ ٱلْمَغْفِرَةِ

Wa maa yazkuroona illaaa any yashaaa'al laah; Huwa ahlut taqwaa wa ahlul maghfirah

Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.