Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Saffat
37

Saffat — Masu Jeri

الصَّافَّاتِ
Makkiyya Aya 182
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَٱلصَّٰٓفَّٰتِ صَفًّۭا

Wassaaaffaati saffaa

Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).

Aya 2

فَٱلزَّٰجِرَٰتِ زَجْرًۭا

Fazzaajiraati zajraa

Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.

Aya 3

فَٱلتَّٰلِيَٰتِ ذِكْرًا

Fattaaliyaati Zikra

Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.

Aya 4

إِنَّ إِلَٰهَكُمْ لَوَٰحِدٌۭ

Inna Illaahakum la Waahid

Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.

Aya 5

رَّبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ ٱلْمَشَٰرِقِ

Rabbus samaawaati wal ardi wa maa bainahumaa wa Rabbul mashaariq

Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.

Aya 6

إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنْيَا بِزِينَةٍ ٱلْكَوَاكِبِ

Innaa zaiyannas samaaa 'ad dunyaa bizeenatinil kawaakib

Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.

Aya 7

وَحِفْظًۭا مِّن كُلِّ شَيْطَٰنٍۢ مَّارِدٍۢ

Wa hifzam min kulli Shaitaanim maarid

Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.

Aya 8

لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلْمَلَإِ ٱلْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍۢ

Laa yassamma 'oona ilal mala il a'alaa wa yuqzafoona min kulli jaanib

Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.

Aya 9

دُحُورًۭا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌۭ وَاصِبٌ

Duhooranw wa lahum 'azaabunw waasib

Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.

Aya 10

إِلَّا مَنْ خَطِفَ ٱلْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُۥ شِهَابٌۭ ثَاقِبٌۭ

Illaa man khatifal khatfata fa atba'ahoo shihaabun saaqib

Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.

Aya 11

فَٱسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَآ ۚ إِنَّا خَلَقْنَٰهُم مِّن طِينٍۢ لَّازِبٍۭ

Fastaftihim ahum ashaddu khalqan am man khalaqnaa; innaa khalaqnaahum min teenil laazib

Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.

Aya 12

بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ

Bal'ajibta wa yaskharoon

Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.

Aya 13

وَإِذَا ذُكِّرُوا۟ لَا يَذْكُرُونَ

Wa izaa zukkiroo laa yazkuroon

Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.

Aya 14

وَإِذَا رَأَوْا۟ ءَايَةًۭ يَسْتَسْخِرُونَ

Wa izaa ra aw Aayatinw yastaskhiroon

Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.

Aya 15

وَقَالُوٓا۟ إِنْ هَٰذَآ إِلَّا سِحْرٌۭ مُّبِينٌ

Wa qaalooo in haazaa illaa sihrum mubeen

Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."

Aya 16

أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًۭا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ

'A-izaa mitnaa wa kunnaa turaabanw wa 'izaaman 'ainnaa lamab'oosoon

"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?

Aya 17

أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ

Awa aabaa'unal awwaloon

"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"

Aya 18

قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَٰخِرُونَ

Qul na'am wa antum daakhiroon

Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."

Aya 19

فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ

Fa innamaa hiya zajra tunw waahidatun fa izaa hum yanzuroon

Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.

Aya 20

وَقَالُوا۟ يَٰوَيْلَنَا هَٰذَا يَوْمُ ٱلدِّينِ

Qa qaaloo yaa wailanaa haazaa Yawmud-Deen

Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."

Aya 21

هَٰذَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ

Haazaa Yawmul Faslil lazee kuntum bihee tukaziboon

Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.

Aya 22

۞ ٱحْشُرُوا۟ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ وَأَزْوَٰجَهُمْ وَمَا كَانُوا۟ يَعْبُدُونَ

Uhshurul lazeena zalamoo wa azwaajahum wa maa kaanoo ya'budoon

Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.

Aya 23

مِن دُونِ ٱللَّهِ فَٱهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلْجَحِيمِ

Min doonil laahi fahdoohum ilaa siraatil Jaheem

Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.

Aya 24

وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْـُٔولُونَ

Wa qifoohum innahum mas'ooloon

Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.

Aya 25

مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ

Maa lakum laa tanaasaroon

Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?

Aya 26

بَلْ هُمُ ٱلْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ

Bal humul Yawma mustaslimoon

Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.

Aya 27

وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَسَآءَلُونَ

Wa aqbala ba'duhum 'alaa ba'diny yatasaaa'aloon

Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.

Aya 28

قَالُوٓا۟ إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ ٱلْيَمِينِ

Qaalooo innakum kuntum taatoonanaa 'anil yameen

Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."

Aya 29

قَالُوا۟ بَل لَّمْ تَكُونُوا۟ مُؤْمِنِينَ

Qaaloo bal lam takoonoo mu'mineen

Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.

Aya 30

وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَٰنٍۭ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًۭا طَٰغِينَ

Wa maa kaana lanaa 'alaikum min sultaanim bal kuntum qawman taagheen

"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."

Aya 31

فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَآ ۖ إِنَّا لَذَآئِقُونَ

Fahaqqa 'alainaa qawlu Rabbinaaa innaa lazaaa'iqoon

"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."

Aya 32

فَأَغْوَيْنَٰكُمْ إِنَّا كُنَّا غَٰوِينَ

Fa aghwainaakum innaa kunnaa ghaaween

"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."

Aya 33

فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍۢ فِى ٱلْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ

Fa innahum Yawma'izin fil'azaabi mushtarikoon

To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.

Aya 34

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِٱلْمُجْرِمِينَ

Innaa kazaalika naf'alu bil mujrimeen

Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.

Aya 35

إِنَّهُمْ كَانُوٓا۟ إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا ٱللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ

Innahum kaanooo izaa qeela lahum laaa ilaaha illal laahu yastakbiroon

Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.

Aya 36

وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوٓا۟ ءَالِهَتِنَا لِشَاعِرٍۢ مَّجْنُونٍۭ

Wa yaqooloona a'innaa lataarikooo aalihatinaa lishaa'irim majnoon

Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?

Aya 37

بَلْ جَآءَ بِٱلْحَقِّ وَصَدَّقَ ٱلْمُرْسَلِينَ

bal jaaa'a bilhaqqi wa saddaqal mursaleen

Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.

Aya 38

إِنَّكُمْ لَذَآئِقُوا۟ ٱلْعَذَابِ ٱلْأَلِيمِ

Innakum lazaaa'iqul 'azaabil aleem

Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.

Aya 39

وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ

Wa maa tujzawna illaa maa kuntum ta'maloon

Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.

Aya 40

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

Illaa 'ibaadal laahil mukhlaseen

Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Aya 41

أُو۟لَٰٓئِكَ لَهُمْ رِزْقٌۭ مَّعْلُومٌۭ

Ulaaa'ika lahum rizqum ma'loom

Waɗannan sunã da abinci sananne.

Aya 42

فَوَٰكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ

Fa waakihu wa hum mukramoon

'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.

Aya 43

فِى جَنَّٰتِ ٱلنَّعِيمِ

Fee jannaatin Na'eem

A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.

Aya 44

عَلَىٰ سُرُرٍۢ مُّتَقَٰبِلِينَ

'Alaa sururim mutaqaa bileen

A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.

Aya 45

يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍۢ مِّن مَّعِينٍۭ

Yutaafu 'alaihim bikaasim mim ma'een

Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.

Aya 46

بَيْضَآءَ لَذَّةٍۢ لِّلشَّٰرِبِينَ

Baidaaa'a laz zatil lish shaaribeen

Farã mai dãɗi ga mashãyan.

Aya 47

لَا فِيهَا غَوْلٌۭ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ

Laa feehaa ghawlunw wa laa hum 'anhaa yunzafoon

A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,

Aya 48

وَعِندَهُمْ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ عِينٌۭ

Wa 'indahum qaasiraatut tarfi 'een

Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.

Aya 49

كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌۭ مَّكْنُونٌۭ

Ka annahunna baidum maknoon

Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.

Aya 50

فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَسَآءَلُونَ

Fa aqbala ba'duhum 'alaa badiny yatasaaa 'aloon

Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.

Aya 51

قَالَ قَآئِلٌۭ مِّنْهُمْ إِنِّى كَانَ لِى قَرِينٌۭ

Qaala qaaa'ilum minhum innee kaana lee qareen

Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."

Aya 52

يَقُولُ أَءِنَّكَ لَمِنَ ٱلْمُصَدِّقِينَ

Yaqoolu a'innnaka laminal musaddiqeen

Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"

Aya 53

أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًۭا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَدِينُونَ

'A-izaa mitnaa wa kunnaa turaabanw wa 'izaaman 'ainnaa lamadeenoon

"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"

Aya 54

قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ

Qaala hal antum muttali'oon

(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"

Aya 55

فَٱطَّلَعَ فَرَءَاهُ فِى سَوَآءِ ٱلْجَحِيمِ

Fattala'a fara aahu fee sawaaa'il Jaheem

Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.

Aya 56

قَالَ تَٱللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ

Qaala tallaahi in kitta laturdeen

Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."

Aya 57

وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّى لَكُنتُ مِنَ ٱلْمُحْضَرِينَ

Wa law laa ni'matu Rabbee lakuntu minal muhdareen

"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."

Aya 58

أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَ

Afamaa nahnu bimaiyiteen

"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."

Aya 59

إِلَّا مَوْتَتَنَا ٱلْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ

Illa mawtatanal oola wa maa nahnu bimu'azzabeen

"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"

Aya 60

إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلْفَوْزُ ٱلْعَظِيمُ

Inna haazaa falya'ma lil'aamiloon

Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.

Aya 61

لِمِثْلِ هَٰذَا فَلْيَعْمَلِ ٱلْعَٰمِلُونَ

Limisli haaza falya'ma lil 'aamiloon

Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.

Aya 62

أَذَٰلِكَ خَيْرٌۭ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ ٱلزَّقُّومِ

Azaalika khairun nuzulan am shajaratuz Zaqqom

Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?

Aya 63

إِنَّا جَعَلْنَٰهَا فِتْنَةًۭ لِّلظَّٰلِمِينَ

Innaa ja'alnaahaa fitnatal lizzaalimeen

Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.

Aya 64

إِنَّهَا شَجَرَةٌۭ تَخْرُجُ فِىٓ أَصْلِ ٱلْجَحِيمِ

Innahaa shajaratun takhruju feee aslil Jaheem

Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.

Aya 65

طَلْعُهَا كَأَنَّهُۥ رُءُوسُ ٱلشَّيَٰطِينِ

Tal'uhaa ka annahoo ru'oosush Shayaateen

Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.

Aya 66

فَإِنَّهُمْ لَءَاكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ

Fa innahum la aakiloona minhaa famaali'oona minhal butoon

To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.

Aya 67

ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًۭا مِّنْ حَمِيمٍۢ

Summa inna lahum 'alaihaa lashawbam min hameem

Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.

Aya 68

ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى ٱلْجَحِيمِ

Summa inna marji'ahum la ilal Jaheem

Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.

Aya 69

إِنَّهُمْ أَلْفَوْا۟ ءَابَآءَهُمْ ضَآلِّينَ

Innahum alfaw aabaaa'ahum daaalleen

Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.

Aya 70

فَهُمْ عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِمْ يُهْرَعُونَ

Fahum 'alaa aasaarihim yuhra'oon

Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.

Aya 71

وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ ٱلْأَوَّلِينَ

Wa laqad dalla qablahum aksarul awwaleen

Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.

Aya 72

وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ

Wa laqad arsalnaa feehim munzireen

Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.

Aya 73

فَٱنظُرْ كَيْفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلْمُنذَرِينَ

Fanzur kaifa kaana 'aaqibatul munzareen

Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.

Aya 74

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

Illaa 'ibaadal laahil mukhlaseen

Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Aya 75

وَلَقَدْ نَادَىٰنَا نُوحٌۭ فَلَنِعْمَ ٱلْمُجِيبُونَ

Wa laqad naadaanaa Noohun falani'mal mujeeboon

Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.

Aya 76

وَنَجَّيْنَٰهُ وَأَهْلَهُۥ مِنَ ٱلْكَرْبِ ٱلْعَظِيمِ

Wa jajainaahu wa ahlahoo minal karbil 'azeem

Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.

Aya 77

وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُۥ هُمُ ٱلْبَاقِينَ

Wa ja'alnaa zurriyyatahoo hummul baaqeen

Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.

Aya 78

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْءَاخِرِينَ

Wa taraknaa 'alaihi fil aakhireen

Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.

Aya 79

سَلَٰمٌ عَلَىٰ نُوحٍۢ فِى ٱلْعَٰلَمِينَ

Salaamun 'alaa Noohin fil 'aalameen

Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.

Aya 80

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

Innaa kazaalika najzil muhsineen

Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Aya 81

إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

Innahoo min 'ibaadinal mu'mineen

Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.

Aya 82

ثُمَّ أَغْرَقْنَا ٱلْءَاخَرِينَ

Summa aghraqnal aakhareen

Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.

Aya 83

۞ وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِۦ لَإِبْرَٰهِيمَ

Wa ina min shee'atihee la Ibraaheem

Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.

Aya 84

إِذْ جَآءَ رَبَّهُۥ بِقَلْبٍۢ سَلِيمٍ

Iz jaaa'a Rabbahoo bi qalbin saleem

A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.

Aya 85

إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِۦ مَاذَا تَعْبُدُونَ

Iz qaala li abeehi wa qawmihee maazaa ta'budoon

A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"

Aya 86

أَئِفْكًا ءَالِهَةًۭ دُونَ ٱللَّهِ تُرِيدُونَ

A'ifkan aalihatan doonal laahi tureedoon

"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"

Aya 87

فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Famaa zannukum bi Rabbil'aalameen

"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"

Aya 88

فَنَظَرَ نَظْرَةًۭ فِى ٱلنُّجُومِ

Fanazara nazratan finnujoom

Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.

Aya 89

فَقَالَ إِنِّى سَقِيمٌۭ

Faqaala inee saqeem

Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."

Aya 90

فَتَوَلَّوْا۟ عَنْهُ مُدْبِرِينَ

Fatawallaw 'anhu mudbireen

Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.

Aya 91

فَرَاغَ إِلَىٰٓ ءَالِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ

Faraagha ilaaa aalihatihim faqaala alaa taakuloon

Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?

Aya 92

مَا لَكُمْ لَا تَنطِقُونَ

Maa lakum laa tantiqoon

"Me ya sãme ku, bã ku magana?"

Aya 93

فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًۢا بِٱلْيَمِينِ

Faraagha 'alaihim darbam bilyameen

Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.

Aya 94

فَأَقْبَلُوٓا۟ إِلَيْهِ يَزِفُّونَ

Fa aqbalooo ilaihi yaziffoon

Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.

Aya 95

قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ

Qaala ata'budoona maa tanhitoon

Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,

Aya 96

وَٱللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ

Wallaahu khalaqakum wa maa ta'maloon

"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"

Aya 97

قَالُوا۟ ٱبْنُوا۟ لَهُۥ بُنْيَٰنًۭا فَأَلْقُوهُ فِى ٱلْجَحِيمِ

Qaalub noo lahoo bun yaanan fa alqoohu fil jaheem

Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."

Aya 98

فَأَرَادُوا۟ بِهِۦ كَيْدًۭا فَجَعَلْنَٰهُمُ ٱلْأَسْفَلِينَ

Fa araadoo bihee kaidan faja 'alnaahumul asfaleen

Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.

Aya 99

وَقَالَ إِنِّى ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّى سَيَهْدِينِ

Wa qaala innee zaahibun ilaa Rabbee sa yahdeen

Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."

Aya 100

رَبِّ هَبْ لِى مِنَ ٱلصَّٰلِحِينَ

Rabbi hab lee minas saaliheen

"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."

Aya 101

فَبَشَّرْنَٰهُ بِغُلَٰمٍ حَلِيمٍۢ

Fabashsharnaahu bighulaamin haleem

Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.

Aya 102

فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ ٱلسَّعْىَ قَالَ يَٰبُنَىَّ إِنِّىٓ أَرَىٰ فِى ٱلْمَنَامِ أَنِّىٓ أَذْبَحُكَ فَٱنظُرْ مَاذَا تَرَىٰ ۚ قَالَ يَٰٓأَبَتِ ٱفْعَلْ مَا تُؤْمَرُ ۖ سَتَجِدُنِىٓ إِن شَآءَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلصَّٰبِرِينَ

Falamma balagha ma'a hus sa'ya qaala yaa buniya inneee araa fil manaami anneee azbahuka fanzur maazaa taraa; qaala yaaa abatif 'al maa tu'maru satajidunee in shaaa'allaahu minas saabireen

To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."

Aya 103

فَلَمَّآ أَسْلَمَا وَتَلَّهُۥ لِلْجَبِينِ

Falammaaa aslamaa wa tallahoo liljabeen

To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.

Aya 104

وَنَٰدَيْنَٰهُ أَن يَٰٓإِبْرَٰهِيمُ

Wa naadainaahu ai yaaaa Ibraheem

Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"

Aya 105

قَدْ صَدَّقْتَ ٱلرُّءْيَآ ۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

Qad saddaqtar ru'yaa; innaa kazaalika najzil muhsineen

"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Aya 106

إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلْبَلَٰٓؤُا۟ ٱلْمُبِينُ

Inna haazaa lahuwal balaaa'ul mubeen

Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.

Aya 107

وَفَدَيْنَٰهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍۢ

Wa fadainaahu bizibhin 'azeem

Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.

Aya 108

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْءَاخِرِينَ

Wa taraknaa 'alaihi fil aakhireen

Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.

Aya 109

سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِبْرَٰهِيمَ

Salaamun 'alaaa Ibraaheem

Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.

Aya 110

كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

Kazaalika najzil muhsineen

Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Aya 111

إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

Innahoo min 'ibaadinal mu'mineen

Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

Aya 112

وَبَشَّرْنَٰهُ بِإِسْحَٰقَ نَبِيًّۭا مِّنَ ٱلصَّٰلِحِينَ

Wa bashsharnaahu bi Ishaaqa Nabiyayam minas saaliheen

Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.

Aya 113

وَبَٰرَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰٓ إِسْحَٰقَ ۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌۭ وَظَالِمٌۭ لِّنَفْسِهِۦ مُبِينٌۭ

Wa baaraknaa 'alaihi wa 'alaaa Ishaaq; wa min zurriyya tihimaa muhsinunw wa zaalimul linafshihee mubeen

Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).

Aya 114

وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

Wa laqad mananna alaa Moosaa wa Haaroon

Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.

Aya 115

وَنَجَّيْنَٰهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ ٱلْكَرْبِ ٱلْعَظِيمِ

Wa najjainaahumaa wa qawmahumaa minal karbil 'azeem

Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.

Aya 116

وَنَصَرْنَٰهُمْ فَكَانُوا۟ هُمُ ٱلْغَٰلِبِينَ

Wa nasarnaahum fakaanoo humul ghaalibeen

Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.

Aya 117

وَءَاتَيْنَٰهُمَا ٱلْكِتَٰبَ ٱلْمُسْتَبِينَ

Wa aatainaahumal Kitaabal mustabeen

Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.

Aya 118

وَهَدَيْنَٰهُمَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلْمُسْتَقِيمَ

Wa hadainaahumus Siraatal Mustaqeem

Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.

Aya 119

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِمَا فِى ٱلْءَاخِرِينَ

Wa taraknaa 'alaihimaa fil aakhireen

Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.

Aya 120

سَلَٰمٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

Salaamun 'alaa Moosaa wa Haaroon

Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.

Aya 121

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

Innaa kazaalika najzil muhsineen

Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Aya 122

إِنَّهُمَا مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

Innahumaa min 'ibaadinal mu'mineen

Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.

Aya 123

وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

Wa inna Ilyaasa laminal mursaleen

Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

Aya 124

إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِۦٓ أَلَا تَتَّقُونَ

Iz qaala liqawmiheee alaa tattaqoon

A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"

Aya 125

أَتَدْعُونَ بَعْلًۭا وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ ٱلْخَٰلِقِينَ

Atad'oona Ba'lanw wa tazaroona ahsanal khaaliqeen

"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"

Aya 126

ٱللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ

Allaaha Rabbakum wa Rabba aabaaa'ikumul awwaleen

"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"

Aya 127

فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ

Fakazzaboohu fa inna hum lamuhdaroon

Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).

Aya 128

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

Illaa 'ibaadal laahil mukhlaseen

Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Aya 129

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْءَاخِرِينَ

Wa taraknaa 'alaihi fil aakhireen

Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.

Aya 130

سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِلْ يَاسِينَ

Salaamun 'alaaa Ilyaaseen

Aminci ya tabbata ga Ilyãs.

Aya 131

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

Innaa kazaalika najzil muhsineen

Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Aya 132

إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

Innahoo min 'ibaadinal mu'mineen

Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

Aya 133

وَإِنَّ لُوطًۭا لَّمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

Wa inna Lootal laminal mursaleen

Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

Aya 134

إِذْ نَجَّيْنَٰهُ وَأَهْلَهُۥٓ أَجْمَعِينَ

Iz najjainaahu wa ahlahooo ajma'een

A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.

Aya 135

إِلَّا عَجُوزًۭا فِى ٱلْغَٰبِرِينَ

Illaa 'ajoozan fil ghaabireen

Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).

Aya 136

ثُمَّ دَمَّرْنَا ٱلْءَاخَرِينَ

Summa dammarnal aakhareen

Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.

Aya 137

وَإِنَّكُمْ لَتَمُرُّونَ عَلَيْهِم مُّصْبِحِينَ

Wa innakum latamurroona 'alaihim musbiheen

Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.

Aya 138

وَبِٱلَّيْلِ ۗ أَفَلَا تَعْقِلُونَ

Wa billail; afalaa ta'qiloon

Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?

Aya 139

وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

Wa inna Yoonusa laminal mursaleen

Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

Aya 140

إِذْ أَبَقَ إِلَى ٱلْفُلْكِ ٱلْمَشْحُونِ

Iz abaqa ilal fulkil mash hoon

A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.

Aya 141

فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ ٱلْمُدْحَضِينَ

Fasaahama fakaana minal mudhadeen

Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.

Aya 142

فَٱلْتَقَمَهُ ٱلْحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٌۭ

Faltaqamahul hootu wa huwa muleem

Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

Aya 143

فَلَوْلَآ أَنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلْمُسَبِّحِينَ

Falaw laaa annahoo kaana minal musabbiheen

To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,

Aya 144

لَلَبِثَ فِى بَطْنِهِۦٓ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ

Lalabisa fee batniheee ilaa Yawmi yub'asoon

Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.

Aya 145

۞ فَنَبَذْنَٰهُ بِٱلْعَرَآءِ وَهُوَ سَقِيمٌۭ

Fanabaznaahu bil'araaa'i wa huwa saqeem

Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.

Aya 146

وَأَنۢبَتْنَا عَلَيْهِ شَجَرَةًۭ مِّن يَقْطِينٍۢ

Wa ambatnaa 'alaihi shajaratam mai yaqteen

Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.

Aya 147

وَأَرْسَلْنَٰهُ إِلَىٰ مِا۟ئَةِ أَلْفٍ أَوْ يَزِيدُونَ

Wa arsalnaahu ilaa mi'ati alfin aw yazeedoon

Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).

Aya 148

فَـَٔامَنُوا۟ فَمَتَّعْنَٰهُمْ إِلَىٰ حِينٍۢ

Fa aamanoo famatta' naahum ilaa heen

Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.

Aya 149

فَٱسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ ٱلْبَنَاتُ وَلَهُمُ ٱلْبَنُونَ

Fastaftihim ali Rabbikal banaatu wa lahumul banoon

Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"

Aya 150

أَمْ خَلَقْنَا ٱلْمَلَٰٓئِكَةَ إِنَٰثًۭا وَهُمْ شَٰهِدُونَ

Am khalaqnal malaaa'i kata inaasanw wa hm shaahidoon

Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?

Aya 151

أَلَآ إِنَّهُم مِّنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَ

Alaaa innahum min ifkihim la yaqooloon

To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.

Aya 152

وَلَدَ ٱللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَٰذِبُونَ

Waladal laahu wa innhum lakaaziboon

"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.

Aya 153

أَصْطَفَى ٱلْبَنَاتِ عَلَى ٱلْبَنِينَ

Astafal banaati 'alal baneen

Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?

Aya 154

مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ

Maa lakum kaifa tahkumoon

Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?

Aya 155

أَفَلَا تَذَكَّرُونَ

Afalaa tazakkaroon

Shin, bã ku tunãni?

Aya 156

أَمْ لَكُمْ سُلْطَٰنٌۭ مُّبِينٌۭ

Am lakum sultaanum mubeen

Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?

Aya 157

فَأْتُوا۟ بِكِتَٰبِكُمْ إِن كُنتُمْ صَٰدِقِينَ

Faatoo bi Kitaabikum in kuntum saadiqeen

To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.

Aya 158

وَجَعَلُوا۟ بَيْنَهُۥ وَبَيْنَ ٱلْجِنَّةِ نَسَبًۭا ۚ وَلَقَدْ عَلِمَتِ ٱلْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ

Wa ja'aloo bainahoo wa bainal jinnati nasabaa; wa laqad 'alimatil jinnatu innahum lamuhdaroon

Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"

Aya 159

سُبْحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ

Subhaanal laahi 'ammaa yasifoon

Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.

Aya 160

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

Illaa 'ibaadal laahil mukhlaseen

Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Aya 161

فَإِنَّكُمْ وَمَا تَعْبُدُونَ

Fa innakum wa maa ta'ubdoon

To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,

Aya 162

مَآ أَنتُمْ عَلَيْهِ بِفَٰتِنِينَ

Maaa antum 'alaihi befaaatineen

Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.

Aya 163

إِلَّا مَنْ هُوَ صَالِ ٱلْجَحِيمِ

Illaa man huwa saalil jaheem

Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.

Aya 164

وَمَا مِنَّآ إِلَّا لَهُۥ مَقَامٌۭ مَّعْلُومٌۭ

Wa maa minnasa illaa lahoo maqaamum ma'loom

"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."

Aya 165

وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلصَّآفُّونَ

Wa innaa llanah nus saaffoon

"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."

Aya 166

وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلْمُسَبِّحُونَ

Wa innaa lanah nul musabbihoon

"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."

Aya 167

وَإِن كَانُوا۟ لَيَقُولُونَ

Wa in kaanoo la yaqooloon

Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,

Aya 168

لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًۭا مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ

Law anna 'indana zikram minal awwaleen

"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."

Aya 169

لَكُنَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

Lakunna 'ibaadal laahil mukhlaseen

"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."

Aya 170

فَكَفَرُوا۟ بِهِۦ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ

Fakafaroo bihee fasawfa ya'lamoon

Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.

Aya 171

وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا ٱلْمُرْسَلِينَ

Wa laqad sabaqat Kalimatunaa li'ibaadinal mursa leen

Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.

Aya 172

إِنَّهُمْ لَهُمُ ٱلْمَنصُورُونَ

Innaa hum lahumul mansooroon

Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.

Aya 173

وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ ٱلْغَٰلِبُونَ

Wa inna jundana lahumul ghaaliboon

Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.

Aya 174

فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍۢ

Fatawalla 'anhum hatta heen

Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.

Aya 175

وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ

Wa absirhum fasawfa yubsiroon

Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.

Aya 176

أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ

Afabi'azaabinaa yasta'jiloon

Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?

Aya 177

فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَآءَ صَبَاحُ ٱلْمُنذَرِينَ

Fa izaa nazala bisaahatihim fasaaa'a sabaahul munzareen

To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.

Aya 178

وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍۢ

Wa tawalla 'anhum hattaa heen

Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.

Aya 179

وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ

Wa absir fasawfa yubsiroon

Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.

Aya 180

سُبْحَٰنَ رَبِّكَ رَبِّ ٱلْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ

Subhaana Rabbika Rabbil 'izzati 'amma yasifoon

Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.

Aya 181

وَسَلَٰمٌ عَلَى ٱلْمُرْسَلِينَ

Wa salaamun 'alalmursaleen

Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.

Aya 182

وَٱلْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Walhamdu lillaahi Rabbil 'aalameen

Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.