Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Zalzala
99

Zalzala — Girgizar Ƙasa

الزَّلۡزَلَةِ
Madaniyya Aya 8
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

إِذَا زُلْزِلَتِ ٱلْأَرْضُ زِلْزَالَهَا

Izaa zul zilatil ardu zil zaalaha

Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.

Aya 2

وَأَخْرَجَتِ ٱلْأَرْضُ أَثْقَالَهَا

Wa akh rajatil ardu athqaalaha

Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.

Aya 3

وَقَالَ ٱلْإِنسَٰنُ مَا لَهَا

Wa qaalal insaanu ma laha

Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"

Aya 4

يَوْمَئِذٍۢ تُحَدِّثُ أَخْبَارَهَا

Yawmaa izin tuhad dithu akhbaaraha

A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.

Aya 5

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوْحَىٰ لَهَا

Bi-anna rabbaka awhaa laha

cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.

Aya 6

يَوْمَئِذٍۢ يَصْدُرُ ٱلنَّاسُ أَشْتَاتًۭا لِّيُرَوْا۟ أَعْمَٰلَهُمْ

Yawma iziy yas durun naasu ash tatal liyuraw a'maalahum

A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.

Aya 7

فَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْرًۭا يَرَهُۥ

Famaiy ya'mal mithqala zarratin khai raiy-yarah

To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.

Aya 8

وَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍۢ شَرًّۭا يَرَهُۥ

Wa maiy-y'amal mithqala zarratin sharraiy-yarah

Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.