Noor
Hausa
Noor / Addu'a / Safiya da Yamma / Azkar na safiya

Azkar na safiya

Safiya da Yamma · addu'o'i 23

Azkar na safiya 0:00
Saurara
1

اللَّهُ لاَ إِلَهَ إِلاَّ هُوَ الْحَيُّ الْقَيُّومُ لاَ تَأْخُذُهُ سِنَةٌ وَلاَ نَوْمٌ لَّهُ مَا فِي السَّمَوَاتِ وَمَا فِي الأَرْضِ مَن ذَا الَّذِي يَشْفَعُ عِنْدَهُ إِلاَّ بِإِذْنِهِ يَعْلَمُ مَا بَيْنَ أَيْدِيهِمْ وَمَا خَلْفَهُمْ وَلاَ يُحِيطُونَ بِشَيْءٍ مِّنْ عِلْمِهِ إِلاَّ بِمَا شَاء وَسِعَ كُرْسِيُّهُ السَّمَوَاتِ وَالْأَرْضَ وَلاَ يَؤُودُهُ حِفْظُهُمَا وَهُوَ الْعَلِيُّ الْعَظِيمُ

Allah, bãbu wani Ubangiji fãce Shi, Rãyayye, Mai tsayuwa da kõme, gyangyaɗi bã ya kãma Shi, kuma barci bã ya kãma Shi, Shi ne da abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa. Wane ne wanda yake yin cẽto a wurinSa, fãce da izninSa? Yana sanin abin da yake a gaba gare su da abin da yake a bãyansu. Kuma bã su kẽwayẽwa da kõme daga ilminSa, fãce da abin da Ya so. KursiyyunSa ya yalwaci sammai da ƙasa. Kuma tsare su bã ya nauyayarSa. Kuma Shi ne Maɗaukaki, Mai girma.

Majiya: Al-Hakim 1 / 562, Sahih at-Targhib wa at-Tarhib 1/273, at-Tabarani.

2

بسم الله الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ ﴿قُلْ هُوَ اللَّهُ أَحَدٌ* اللَّهُ الصَّمَدُ* لَمْ يَلِدْ وَلَمْ يُولَدْ* وَلَمْ يَكُن لَّهُ كُفُواً أَحَدٌ﴾. بسم الله الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ ﴿قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ الْفَلَقِ* مِن شَرِّ مَا خَلَقَ* وَمِن شَرِّ غَاسِقٍ إِذَا وَقَبَ* وَمِن شَرِّ النَّفَّاثَاتِ فِي الْعُقَدِ* وَمِن شَرِّ حَاسِدٍ إِذَا حَسَدَ﴾. بسم الله الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ ﴿قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ النَّاسِ* مَلِكِ النَّاسِ* إِلَهِ النَّاسِ* مِن شَرِّ الْوَسْوَاسِ الْخَنَّاسِ* الَّذِي يُوَسْوِسُ فِي صُدُورِ النَّاسِ* مِنَ الْجِنَّةِ وَ النَّاسِ﴾ (ثلاث مرات )

Ka ce: "Shi ne Allah Makaɗaĩci." "Allah wanda ake nufin Sa da buƙata." "Bai haifa ba, kuma ba a haife Shi ba." "Kuma babu ɗaya da ya kasance tamka a gare Shi." Ka ce "ina neman tsari ga Ubangijin safiya" "Daga sharrin abin da Ya halitta." "Da sharrin dare, idan ya yi duhu." "Da sharrin mãtã mãsu tõfi a cikin ƙulle-ƙulle." "Da sharrin mai hãsada idan ya yi hasada." Ka ce "Ina nẽman tsari ga Ubangijin mutãne." "Mamallakin mutane." "Abin bautãwar mutãne." "Daga sharrin mai sanya wasuwãsi, mai ɓoyewa." "Wanda ke sanya wasuwãsi a cikin ƙirãzan mutane." "Daga aljannu da mutane."

Majiya: Al-Ikhlas:1-4. Al-Falaq:1-5. An-Nas:1-6, Abu Dawud 4/322, At-Tirmizi 5/567, Sahih At-Tirmizi 3/182.

3

أَصْبَحْنَا وَأَصْبَحَ الْمُلْكُ لِلَّهِ, وَالْحَمْدُ لِلَّهِ, لاَ إِلَهَ إلاَّ اللَّهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ, لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ, رَبِّ أَسْأَلُكَ خَيْرَ مَا فِي هَذَا الْيَوْمِ وَخَيرَ مَا بَعْدَهُ, وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا فِي هَذَا الْيَوْمِ وَشَرِّ مَا بَعْدَهُ, رَبِّ أَعُوذُ بِكَ مِنَ الْكَسَلِ وَسُوءِ الْكِبَرِ, رَبِّ أَعُوذُ بِكَ مِنْ عَذَابٍ فِي النَّارِ وَعَذَابٍ فِي الْقَبْرِ

un wayi gari kuma mulki na Allah ne kuma godiya ta tabbata ga Allah Babu wani Ubangiji sai shi shi kadai bashida abokin tarayya kuma godiya tasa ce kuma mai iko ne akan komai Ubangiji ina rokon ka Alkairin wannan rana da alkairin abinda yake bayanta kuma ina neman tsarinka daga sharrin wannan rana da abinda yake bayanta Ubangiji ina neman tsarinka daga Kasala da Mummunan girman kai, Ubangiji ina neman tsarinka daga Azabar wuta da kuma Azabar Kabari

Majiya: Muslim 4/2088.

4

اللَّهُمَّ بِكَ أَصْبَحْنَا, وَبِكَ أَمْسَيْنَا, وَبِكَ نَحْيَا, وَبِكَ نَمُوتُ وَإِلَيْكَ النُّشُورُ

Ya Ubangiji dakai muka wayi gari kuma dakai mukayi yammaci, kuma dakai muke Rayuwa kuma dakai muka mutuwa kuma gareka muke tashi

Majiya: Sahih At-Tirmizi 3/142.

5

اللَّهُمَّ أَنْتَ رَبِّي لَا إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ, خَلَقْتَنِي وَأَنَا عَبْدُكَ, وَأَنَا عَلَى عَهْدِكَ وَوَعْدِكَ مَا اسْتَطَعْتُ, أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا صَنَعْتُ, أَبُوءُ لَكَ بِنِعْمَتِكَ عَلَيَّ, وَأَبُوءُ بِذَنْبِي فَاغْفِرْ لِي فَإِنَّهُ لاَ يَغْفِرُ الذُّنوبَ إِلاَّ أَنْتَ

Ya Ubangiji kaine ubangiji na babu wani Ubangiji sai kai kai ka halicce ni kuma ni bawanka ne kuma ina nan akan alkaarinka gwargwadon iko ina neman tsarinka daga abinda nayi kuma ina furuci da ni'amar da kayi mun kuma ina furuci da zunubaina kayi mun gafara babu mai gafarta zunubai sai kai kadai

Majiya: Al-Bukhari 7/150, An-Nasa'i, At-Tirmizi.

6

اللَّهُمَّ إِنِّي أَصْبَحْتُ أُشْهِدُكَ, وَأُشْهِدُ حَمَلَةَ عَرْشِكَ, وَمَلاَئِكَتَكَ, وَجَمِيعَ خَلْقِكَ, أَنَّكَ أَنْتَ اللَّهُ لَا إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ وَحْدَكَ لاَ شَرِيكَ لَكَ, وَأَنَّ مُحَمَّداً عَبْدُكَ وَرَسُولُكَ (أربع مرات)

Ya Ubangiji Ni na wayi gari ina shaidawa da kai kuma ina shaidawa da wadanda suke dauke da Al'arshinka da Mala;ikunka da baki dayan halittunka babu wani Ubangiji sai kai kadai baka da abokin tarayya, kuma Annabi muhammadu Bawanka kuma kuma Manzonka ( Sau Hudu)

Majiya: Abu Dawud 4/317, An-Nasa'i, Ibn As-Sunni.

7

اللَّهُمَّ مَا أَصْبَحَ بِي مِنْ نِعْمَةٍ أَوْ بِأَحَدٍ مِنْ خَلْقِكَ فَمِنْكَ وَحْدَكَ لاَ شَرِيكَ لَكَ, فَلَكَ الْحَمْدُ وَلَكَ الشُّكْرُ

Ya Ubangiji abinda Muka wayi gari da shi na Ni'ama ko wani daga cikin halittarka to daga gareka ne kai kadai bakada abokin tarayya, godiya ta tabbata a gareka kuma da yabo

Majiya: Abu Dawud 4/318, Ibn As-Sunni (Hadith no. 41), Ibn Hibban (Hadith no. 2361).

8

اللَّهُمَّ عَافِنِي فِي بَدَنِي, اللَّهُمَّ عَافِنِي فِي سَمْعِي, اللَّهُمَّ عَافِنِي فِي بَصَرِي, لاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ. اللَّهُمَّ إِنِّي أَعُوذُ بِكَ مِنَ الْكُفْرِ, وَالفَقْرِ, وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ عَذَابِ القَبْرِ, لاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ (ثلاث مرات)

Ya Ubangiji ka bani lafiya a jikina Ya Ubangiji ka bani lafiya cikin jina ya Ubangiji ka bani lafiya cikin gani na Ya Ubangiji ina neman tsarinka daga Kafirci da kuma talauci, kuma ina neman tsarin ka daga Azabar kabari babu wani ubangiji sai kai ( Sau uku )

Majiya: Abu Dawud 4/324, Ahmad 5/42, An-Nasa'i, Ibn As-Sunni (Hadith no. 69), Ibn Hibban (Hadith no. 2361).

9

حَسْبِيَ اللَّهُ لاَ إِلَهَ إِلاَّ هُوَ عَلَيهِ تَوَكَّلتُ وَهُوَ رَبُّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ (سبع مرات)

Allah ya ishe ni Babu wani Ubangiji sai shi gare shi na dogara kuma shi ne ubangijin Al'arshi mai girma ( Sau bakwai )

Majiya: Ibn As-Sunni (no. 71), Abu Dawud 4/321, Ibn As-Sunni.

10

اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ الْعَفْوَ وَالْعَافِيَةَ فِي الدُّنْيَا وَالآخِرَةِ, اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ الْعَفْوَ وَالْعَافِيَةَ: فِي دِينِي وَدُنْيَايَ وَأَهْلِي, وَمَالِي, اللَّهُمَّ اسْتُرْ عَوْرَاتِي, وَآمِنْ رَوْعَاتِي, اللَّهُمَّ احْفَظْنِي مِنْ بَينِ يَدَيَّ, وَمِنْ خَلْفِي, وَعَنْ يَمِينِي, وَعَنْ شِمَالِي, وَمِنْ فَوْقِي, وَأَعُوذُ بِعَظَمَتِكَ أَنْ أُغْتَالَ مِنْ تَحْتِي

Ya Ubangiji ina rokonka afuwa da lafiya a Dauniya da lahira Ya Ubangiji ina rokonka afuwa da da lafiya, a cikin Acikin Duniya ta da Ahalina da Dukiya ta Ya Ubangiji ka Suturta Al'aura ta kuma ka amintar da ni abinda nake tsoro, Ya Ubangiji ka kiyaye ni a gabana da baya na, da dama na da haguna da sama na da kasa na kuma ina neman tsari da girmanka kada a hallaka ni ta karkashina

Majiya: Sahih Ibn Majah 2/332, Abu Dawud.

11

اللَّهُمَّ عَالِمَ الغَيْبِ وَالشَّهَادَةِ فَاطِرَ السَّمَوَاتِ وَالْأَرْضِ, رَبَّ كُلِّ شَيْءٍ وَمَلِيكَهُ, أَشْهَدُ أَنْ لاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ, أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ نَفْسِي, وَمِنْ شَرِّ الشَّيْطانِ وَشَرَكِهِ, وَأَنْ أَقْتَرِفَ عَلَى نَفْسِي سُوءاً, أَوْ أَجُرَّهُ إِلَى مُسْلِمٍ

Ya Ubangiji Masanin fake da fili wanda ya halicci sama da kasa ubangijin komai kuma mai mulkinsu na shaida babu wani ubnagiji sai kai ina neman tsarinka daga sharrin kaina da sharrin shaidan da mataimakansa ko kuma inyi wani zunubi ko injawo shi ga wani Musulmi

Majiya: Sahih At-Tirmizi 3/142, Abu Dawud.

12

بِسْمِ اللَّهِ الَّذِي لاَ يَضُرُّ مَعَ اسْمِهِ شَيْءٌ فِي الْأَرْضِ وَلاَ فِي السّمَاءِ وَهُوَ السَّمِيعُ الْعَلِيمُ (ثلاث مرات)

Da sunan Allah wanda babu abinda yake utarwa da fadin sunansa a cikin sama ne ko kuma a kasa kuma shi mai ji ne masani

Majiya: Abu Dawud 4/323, At-Tirmizi 5/465, Ibn Majah 2/332, Ahmad.

13

رَضِيتُ بِاللَّهِ رَبَّاً, وَبِالْإِسْلاَمِ دِيناً, وَبِمُحَمَّدٍ صلى الله عليه وسلم نَبِيّاً (ثلاث مرات)

Na yarda da Allah shi ne Ubangiji kuma Musulunci shi ne Addini kuma Annabi Muhammadu shi ne Annabi (Sau Uku)

Majiya: Ahmad 4/ 337, An-Nasa'i, Ibn As-Sunni (no. 68), At-Tirmizi 5/465.

14

يَا حَيُّ يَا قَيُّومُ بِرَحْمَتِكَ أَسْتَغيثُ أَصْلِحْ لِي شَأْنِيَ كُلَّهُ وَلاَ تَكِلْنِي إِلَى نَفْسِي طَرْفَةَ عَيْنٍ

Ya rayayye tsayyae da kansa ina neman agajinka da rahamarka ka inganta mun al'amura na baki daya kuma kada ka barni da kaina ko daidai da kiftawar Ido

Majiya: Al-Hakim 1/545.

15

أَصْبَحْنَا وَأَصْبَحَ الْمُلْكُ لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ, اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ خَيْرَ هَذَا الْيَوْمِ:فَتْحَهُ, وَنَصْرَهُ, وَنورَهُ, وَبَرَكَتَهُ, وَهُدَاهُ, وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا فِيهِ وَشَرِّ مَا بَعْدَهُ

Mun wayi gari kuma mulki yana hannun Allah Ina rokonka Alkairin wannan rana budinta da Nasararta da haskenta da albarkarta da kuma shiriyarta, kuma ina neman tsarinka daga sharrinta da sharrin duk abinda yake cikin ta da sharrin abinda yake bayanta

Majiya: Abu Dawud 4/322.

16

أَصْبَحْنا عَلَى فِطْرَةِ الْإِسْلاَمِ, وَعَلَى كَلِمَةِ الْإِخْلاَصِ, وَعَلَى دِينِ نَبِيِّنَا مُحَمَّدٍ صلى الله عليه وسلم, وَعَلَى مِلَّةِ أَبِينَا إِبْرَاهِيمَ, حَنِيفاً مُسْلِماً وَمَا كَانَ مِنَ الْمُشرِكِينَ

Mun wayi gari akan turbar Addinin Musulunci, kuma kan kalmar tsarkake Addini kuma kan Addinin Annabinmu Muhammad kuma kan tafarkin Babanmu Annabi Ibrahim wanda ya tsaya kyam kan Addini bai kasance cikin masu shika ba

Majiya: Ahmad 3/406-7, 5/123, An-Nasa'i, At-Tirmizi 4/209.

17

سُبْحَانَ اللَّهِ وَبِحَمْدِهِ (مائة مرة)

Tsarki ya tabbata ga Allah da kuma godiya ( Sau dari )

Majiya: Muslim 4/2071.

18

لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ, لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ, وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ (عشر مرات أو مرة واحدة عند الكسل)

Babu wani Ubangiji da ya cancanci a bauta masa da gaskiya sai Allah shi kadai wanda bashi da Abokin tarayya Mulki nasa ne haka ma godiya kuma shi mai Iko ne akan komai ( Sau goma) ko ( Sau daya in ya gaji)

Majiya: An-Nasa'i, Abu Dawud 4/319, Ibn Majah, Ahmad 4/60.

19

لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ, وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ, لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ (مائة مرة)

Babu wani Ubangiji da ya cancanci a bauta masa da gaskiya sai Allah shi kadai bashi da abokin tarayya Mulki nasa ne haka ma godiya kuma shi mai iko ne akan komai

Majiya: Al-Bukhari 4/95, Muslim 4/2071.

20

سُبْحَانَ اللَّهِ وَبِحَمْدِهِ: عَدَدَ خَلْقِهِ, وَرِضَا نَفْسِهِ, وَزِنَةَ عَرْشِهِ, وَمِدَادَ كَلِمَاتِهِ (ثلاث مرات)

Tsarki ya tabbata ga Allah da godiyarsa, yawan halittarsa da kuma yardarsa, da kuma nauyin Al'arshinsa da kuma yawan Kalmominsa, ( Sau Uku safe )

Majiya: Muslim 4/2090.

21 AI

اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ عِلْماً نَافِعاً, وَرِزْقاً طَيِّباً, وَعَمَلاً مُتَقَبَّلاً

Ya Allah, ina rokonka ilimi mai amfani, da arziki mai kyau, da aiki da aka karɓa.

Majiya: Ibn As-Sunni (Hadith no. 54), Ibn Majah (Hadith no. 925).

22

أَسْتَغْفِرُ اللَّهَ وَأَتُوبُ إِلَيْهِ (مائة مرة في اليوم)

Ina neman gafarar Allah kuma ina tuba izuwa gare shi ( Sau dai)

Majiya: Al-Bukhari, Muslim 4/2075.

23

اللَّهُمَّ صَلِّ وَسَلِّمْ عَلَى نَبَيِّنَا مُحَمَّدٍ (عشر مرات)

Yace: Allah kayi salati da tsira ga Anabinmu Muhammad ( Sau goma )

Majiya: At-Tabrani, Sahih at-Targhib wa at-Tarhib 1/273.

AI

Rubutun Larabci da tushensa amintattu ne. Abubuwan da aka yi wa alama da “AI” an fassara su ta na’ura zuwa harshenka kuma suna iya ƙunsar kurakurai — Larabci ne ma’auni. Danna “Kai rahoto” a kan kowane abu don bayar da rahoton matsala.