اللَّهُمَّ أَعِذْهُ مِنْ عَذَابِ القَبْرِ, وإن قال: اللَّهُمَّ اجْعَلْهُ فَرَطاً وَذُخْراً لِوَالِدَيْهِ, وَشَفِيعاً مُجَاباً, اللَّهُمَّ ثَقِّلْ بِهِ مَوَازِينَهُمَا, وَأَعْظِمْ بِهِ أُجورَهُمَا, وَأَلْحِقْهُ بِصَالِحِ الْمُؤْمِنِينَ, وَاجْعَلْهُ فِي كَفَالَةِ إِبْرَاهِيمَ, وَقِهِ بِرَحْمَتِكَ عَذَابَ الْجَحِيمِ, وَأَبْدِلْهُ دَاراً خَيْراً مِنْ دَارِهِ, وَأَهْلاً خَيْراً مِنْ أَهْلِهِ, اللَّهُمَّ اغْفِرْ لِأَسْلاَفِنَا, وَأَفْرَاطِنَا, وَمَنْ سَبَقَنَا بِالْإِيمَانِ (فَحَسَنٌ)
Ya Allah, ka tsare shi daga azabar kabari. (Yana da kyau kuma a ce:) Ya Allah, ka sanya shi ga iyayensa magabaci, da tanadi, da maceci wanda ake karɓar cetonsa. Ya Allah, ka nauyaya ma'aunansu da shi, ka kuma girmama ladansu da shi, ka haɗa shi da muminai salihai, ka sanya shi a cikin kulawar Ibrahim, ka tsare shi da rahamarka daga azabar Jahim, ka kuma musanya masa gida mafi alheri daga gidansa da iyali mafi alheri daga iyalinsa. Ya Allah, ka gafarta wa magabatanmu, da 'ya'yanmu (da suka mutu), da waɗanda suka riga mu zuwa ga imani.
Majiya: Ibn Qudamah, Al-Mughni 3/416.