Noor
Hausa
Noor / Alƙur'ani / Humaza
104

Humaza — Mai Zunɗe

الهُمَزَةِ
Makkiyya Aya 9
Saurari sura 0:00
Saurara · Mishary Rashid Alafasy

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

Aya 1

وَيْلٌۭ لِّكُلِّ هُمَزَةٍۢ لُّمَزَةٍ

Wai lul-li kulli hu mazatil-lumaza

Bone ya tabbata ga duk mai nune, mai zunɗe (mai raɗa).

Aya 2

ٱلَّذِى جَمَعَ مَالًۭا وَعَدَّدَهُۥ

Al-lazi jama'a maalaw wa'addadah

Wanda ya tara dũkiya, kuma ya mayar da ita abar tattalinsa.

Aya 3

يَحْسَبُ أَنَّ مَالَهُۥٓ أَخْلَدَهُۥ

Yahsabu anna maalahu akhladah

Yana zaton cẽwa dũkiyarsa za ta dawwamar da shi.

Aya 4

كَلَّا ۖ لَيُنۢبَذَنَّ فِى ٱلْحُطَمَةِ

Kalla layum ba zanna fil hutamah

A'aha! Lalle ne zã a jẽfa shi a cikin Huɗama.

Aya 5

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْحُطَمَةُ

Wa maa adraaka mal-hutamah

Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa Huɗama?

Aya 6

نَارُ ٱللَّهِ ٱلْمُوقَدَةُ

Narul laahil-mooqada

Wutar Allah ce wadda ake hurawa.

Aya 7

ٱلَّتِى تَطَّلِعُ عَلَى ٱلْأَفْـِٔدَةِ

Al latee tat tali'u 'alalafidah

Wadda take lẽƙãwa a kan zukata.

Aya 8

إِنَّهَا عَلَيْهِم مُّؤْصَدَةٌۭ

Innaha 'alaihim moosada

Lalle ne ita abar kullẽwa cea kansu.

Aya 9

فِى عَمَدٍۢ مُّمَدَّدَةٍۭ

Fee 'amadim-mu mad dadah

A cikin wasu ginshiƙai mĩƙaƙƙu.